Dangote ya gina sabon kamfanin sarrafa shinkafa a Arewa

Dangote ya gina sabon kamfanin sarrafa shinkafa a Arewa

Shugaban kamfanin Dangote, Aliko Dangote yace zai taimaka wa manoman shinkafa 15,000 a kasa Najeriya da kayayyakin noma da taki.

Dangote ya gina kamfanin sarrafa shinkafa a karamar hukumar Goronyo dake jihar Sokoto.

Dangote ya gina sabon kamfanin sarrafa shinkafa a Arewa
Dangote ya gina sabon kamfanin sarrafa shinkafa a Arewa

Ya kara da cewa kamfaninsa za ta fara da manoma 15,000 ne sannan a hankali ta na kara yawan manoman.

Yace zai kuma taimakawa manoman rake a jihar.

KU KARANTA: Yanzu-Yanzu: Sako daga fadar shugaban kasa

Bayan haka Dangote ya ce kamfaninsa za ta wadatar da kayan noma wa manoman kamarsu maganin feshi,ragar kare shinkafa daga tsuntsaye, irin shukawa da dai sauran su.

Ya kara yi wa manoman albishir cewa kamfanin na sa za ta koyar da manoman yankin yadda za su yi amfani da dabarun noma na zamani sannan kuma su kamfanin za ta siya shinkafar bayan sun noma.

Daga karshe ya ce wannan kawancen da za su hada da manoman zai taimaka wurin samar da aiki wa mutanen jihar daga mutane 15,000 zuwa mutane 50,000.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng