Kun ji abunda za'ayiwa karuwan Abuja?

Kun ji abunda za'ayiwa karuwan Abuja?

- Yadda matsalar Karuwanci ke kara muni a Abuja babban birnin Najeriya al’amarin da ya sa Gwamnati ta sake kaddamar da kwamiti don kawar da wannan annoba.

- An dai kaddamar da kwamitin ne don shawo kan matsalar karuwancin da yanzu haka ta zama ruwan dare a kusan dukkan lunguna da sakuna na fadin birnin tarrayyar.

Kun ji abunda za'ayiwa karuwan Abuja?
Kun ji abunda za'ayiwa karuwan Abuja?

Kwamitin dai ya kunshin manyan mutane da kuma masu ruwa da tsaki a harkar tsaro dama sauran sannan gwamnati da dama.

A wani labarin kuma, Gwamnatin hadin gwiwar Austria ta amince ta hana mata saka burka a wurin taruwar jama'a kamar makarantu da kotuna.

Kasar tana kuma duba yiwuwar hana ma'aikatan kasar saka dankwali da wasu tufafi masu alaƙa da addini.

Ana ganin wannan shawara a matsayin wani yunƙurin daƙile 'yancin da jam'iyyar masu ra'ayin rikau, wanda dan takararsu ya sha kaye da kyar a zaben shugaban kasar na watan da ya gabata ke ci gaba da samu.

A makon da ya gabata ne gamayyar jam'iyyu masu matsakaicin ra'ayi suka kusa rugujewa sakamakon wani rikici a kan wata yarjejeniya game da makomar gwamnatin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: