Kungiyar malamai makaranta za ta fara sabon yajin aiki

Kungiyar malamai makaranta za ta fara sabon yajin aiki

Kungiyar malamai makarantun Polytechnics (ASUP) ta fara gargadin yajin aiki na rana 5.

Kungiyar malamai
Kungiyar malamai makarantun Polytechnics (ASUP)

Yau ranar Litinin, 30 ga watan Disamba ne kungiyar malamai makarantun Polytechnics (ASUP) ta fara gargadin yajin aiki na rana 5 bayan wa'adin da ta yi wa gwamnatin tarayya ta kawo karshe.

Jaridar The Nation ra rahoto cewa kungiyar malamai makarantun Polytechnics ta kasa (ASUP) za ta fara gargadin yajin aiki na mako daya a yau, 30 ga watan Janairu.

KU KARANTA KUMA: ‘Yan bindiga sun hallaka mutane 5 a inda suka bude wa wata masallaci wuta

Malamai sun dauki wannan mataki ne domin nuna rashin amincewarsu da gwamnatin kasar a kan yarjejeniyar ta da ƙungiyar da kuma talafawa makarantun Polytechnic.

Shugaban hukumar Comrade Usman Dutse ya ce wa’adin da ƙungiyar ta ba gwamnatin tarayya ta shige a watan Disamba 2006 da ta gabata ba tare da wata kwakwaran bayyani daga gwamnati.

KU KARANTA KUMA: Rundunar sojojin kasar Najeriya ta mamaye ko’ina a Gambia

Ya ce wannan matakin gwamnati ya bar su ba tare da wata zabi ba ila su soma gargadi yajin aiki na kwana 5.

Ku kasance tare da mu@ https://www.facebook.com/naijcomhausa

http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng