Kulop din Barcelona ta yi hasarar Busquets saboda rauni

Kulop din Barcelona ta yi hasarar Busquets saboda rauni

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta yi babban hasarar dan wasanta Sergio Busquets bayan da ya ji rauni a dunduniyarsa a karawarsu da kulob Eibar a ranar Lahadi a bayan sun ci 4 - 0

Kulop din Barcelona ta yi hasarar Busquets saboda rauni
Kulop din Barcelona ta yi hasarar Busquets saboda rauni

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta ga samu, ta kuma ga rashi bayan da ta lallasa Eibar ta ci 4 da nema, a karawarsu na ranar Lahadi, amma kuma ta yi hasarar Sergio Busquets wanda zai dade bai buga kwallo ba bayan raunin da ya ji a yayin karawar.

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta yi babban hasarar dan wasanta Sergio Busquets bayan da ya ji rauni a dunduniyarsa a karawarsu da kulob Eibar a ranar Lahadi a bayan sun ci 4 - 0

Dan wasa Sergio mai shekara 28 da haihuwa, wanda kuma tauraruwarsa ke haske a Barcelona, an fita da shi ranga-ranga daga fili a gadon daukar maras lafiya na tafi-da-gidanka, bayan kimanin mintuna 8 da soma wasa, bayan sun yi taho mu gama da Gonzalo Escalente.

Sakamakon gwaje-gwajen likita ya nuna cewa, Sergio dan wasan mai buga tsakiya, ya gurde kafarsa ne a inda dunduniyarsa ta tabu, kuma da alamu zai dade yana jinya kafin ya koma buga kwallo.

Wasu rahotanni daga Spain na cewa, dole ce za ta sa a jingine dan wasan na tsawon akalla makonni biyu, wanda hakan zai sa ba za a buga wasan kusa-da-na-kusa da na karshe ba watau kwata final, na gasar Copa del Rey da shi ba, a inda kulop dinsa zai kara da Real Sociedad a ranar Alhamis.

Raunin kuma ya haddasa masa rashin samun dama taka leda a karawar da kulop din sa zai yi a gasar La Liga, a in da za su kara da Real Betis, da Athletic Bilbao, sai dai mai horas da ‘yan wasan Barcelonan Luis Enrique na fatan Sergio zai murmure kafin karawarsu da kulop din PSG a gasar cin kofin zakarun turai wanda za a buga 14 ga watan Fabarairu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: