INNALILAHI WAINAILAIHI RAJIHUN: Tsoho gwamna jihar Niger ya rigamu gidan gaskiya

INNALILAHI WAINAILAIHI RAJIHUN: Tsoho gwamna jihar Niger ya rigamu gidan gaskiya

Tsohon gwamnan jihar Niger injiniya Abdulkadir Kure ya rasu a wata asibiti a kasar Jamus.

Allah ya wa tsoho gwamnan jihar Niger injiniya Abdulkadir Kure rasuwa a wata asibiti a kasar Jamus.

An samu wannan sanarwa ne daga iyalan shi marigayin tsohon gwamnan a cewan su Allah ya masa cikawa ne a wata babban asibiti ta kasar Jamus.

Wata rohoto daga jaridan Nation na cewa an kai wannan tsohon gwamna kasan waje a mako da ya gabata sanadiyan wata rashin lafiya.

Marigayin ya yi wa’adin gwamnati jihar Niger zo biyu daga shekara 1999 har zuwa 2007.

Gwamnan na 12 a jerin tsofofin gwamnonin jihar Niger, kuma yana na 3 a cikin tsofofin zababbu gwamnonin farar hula bayan mai martaba sarki Awwal Ibrahim daga shekara 1979 – 1983 da dokta Musa Inuwa daga shekara 1992 – 1993.

A cikin furucin kwamishinan bayanai, al'adu da yawon shakatawa, Jonathan Vatsa, a garin Minna babban birnin jihar Niger a daren ranar lahadi, a watan Janairu 6, 2017. Gwamnatin jihar ta sanad da ranaku uku na zaman makoki.

A cewar kwamishinan, gwamnan jihar Niger Abubakar Bello ya ba maikatan jihar Niger hutu a ranar jana’izan tsohon gwamnan saboda jama’a su samu hallarta bikin jana’izan.

Ku kasance tare da mu@ https://www.facebook.com/naijcomhausa da http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: