Jerin makarantun da yayan Buhari suka yi karatu a kasashen waje

Jerin makarantun da yayan Buhari suka yi karatu a kasashen waje

Duk da irin zantuttukan da ake dangantawa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari na siyasa, amma shugaban bai yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da yayansa sun samu karatu ingantacce kamar yadda kamata.

Jerin makarantun da yayan Buhari suka yi karatu a kasashen waje
Shugaba Buhari da iyalansa

Cikin wani sharhi da jaridar Premium Times tayi ma littafin tarihin shugaban kasa Muhammadu Buhari wanda wani bature farfesa John Paden ya wallafa “Muhammadu Buhari: The Challenges of Leadership in Nigeria” an gano makarantun da yayan shugaba Buhari suka je, dukkansu,

1- Fatima: An haifi Fatima a shekarar 1975, inda tayi karatun ta a makarantar firamaren sojojin sama dake tsibirin Victoria jihar Legas, sa’annan tayi sakandaren kwalejin gwamnati dake Kaduna, sait wuce jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria, inda ta yi karatun gaba da digiri a cibiyar kasuwanci dake Stratford, kasar Birtaniya.

KU KARANTA:Buhari ne gwani na – Inji shugaban kasar Guinea Bissau

2- Nana Hadiza: an haifi Hadiza a ranar 23 ga watan Yuli na shekarar 1981, inda tayi karatuttkanta a Essence International School dake Kaduna; Cobham Hall, Kent, United Kingdom; jami’ar Buckingham dake Birtaniya; sai cibiyar koyar da malamai ta Kaduna, sa’annan ta kara da digiri na biyu a fannin sanin alakar kasashe, kuma ta yi karatu a kwalejin kimiyya da fasaha na Kaduna.

3- Safinatu: An haife ta a ranar 13 ga watan Oktoba inda tayi karatuttkanta a Essence International School dake Kaduna; Cobham Hall, Kent, United Kingdom; jami’ar Plymouth dake Birtaniya, a yanzu kuma tana jami’ar Arden duk a kasar Birtaniya.

4- Halima: Halima itace babbar yarinyar Aisha Buhari, wanda aka haifeta a ranar 8 ga watan Oktoba 1990, tayi karatu a International School, Kaduna; sakandaren British School dake Lome, Togo; kwalejin Bellerby dake Brighton,kasar Ingila; sai jami’ar Leicester dake Ingila , sai kuma makarantar horar da lauyoyi dake Lagos.

5- Yusuf Buhari: Yusuf Buhari yayi karatu a a International School, Kaduna; sakandaren British School dake Lome, Togo; kwalejin Bellerby dake Brighton,kasar Ingila sai ya tafi jami’ar Surrey a Ingila.

6- Zahra: an haifi Zarah a 1994, 18 ga watan Disamba, tayi karatu a International School, Kaduna; sakandaren British School dake Lome, Togo; kwalejin Bellerby dake Brighton,kasar Ingila sai ta tafi jami’ar Surrey a Ingila.

7- Aisha (Hanan): An haife ta a ranar 30 ga watan Agusta 1998, tayi karatu a Kaduna International School.

8- Noor (Amina): AN haife ta a ranar 14 ga watan Satumba 2004, a yanzu tana karatu a Kaduna International School.

Idan ba’a manta ba a shekarar 2012 ne babban yarinyar shugaba Buhari ta rasu, Zulaihat sanadiyyar ciwon sickler. A baya ma an taba samun yaron shugaba Buhari Musa daya rasu tun yana jariri.

Zaku iya samun labaran mu a nan ko a nan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng