Majalisa na nema a kafa Kotun Ikiliziya

Majalisa na nema a kafa Kotun Ikiliziya

Majalisa na nema a kafa Kotun Ikiliziya
Majalisa na nema a kafa Kotun Ikiliziya

Wani Dan Majalisa Wakilai ta Tarayya mai suna Hon. Gyang Dung daga Jihar Plateau ya kawo wani kudiri zuwa Majalisar Kasar inda yake nema a kafa Kotun Kirista a fadin Kasar nan. Watau dai wannan zai yi daidai da kamar Kotun Shari’ah na Musulunci.

Yanzu dai haka wannan kudiri na kafa Kotun Ikilisiya ya samu tsallake mataki na biyu a Fadar Majalisar. Hon. Gyang Dung na PDP da ke wakiltar mazabar Plateau ne ya gabatar da kudirin tare da wasu ‘Yan Majalisa 8.

KU KARANTA: Patience ta na neman rai hannun Majalisa

Dan Majalisan yace idan har an kafa wannan Kotu, za ta zama tana aiki musamman ga abubuwan da suka shafi Addinin Kirista. Hon. Dung ya bayyanawa manema labarai cewa Kotun ba za tayi aiki a kan wanda bai yadda da Ikiliziya da Addinin Kirista ba.

Sai anyi wa dokar Kasar nan garambawul dai kafin a shigar da wannan kudiri cikin dokar tsarin mulkin Kasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng