Sarki Mohammed VI na Morocco ya ziyarci Najeriya

Sarki Mohammed VI na Morocco ya ziyarci Najeriya

Sarki Mohammed VI na Morocco ya isa kasar Najeriya a ranar Alhamis, 1 ga watan Disamba, don wani ziyarar aiki.

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya tarbi sarkin sannan kuma zai ziyarci shugaban kasa Muhammadu Buhari a yau a fadar shugaban kasa Abuja.

Sarki Mohammed VI na Morocco ya ziyarci Najeriya
Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya tarbi sarki Mohammed VI na Morocco a filin jirgin sama

A farko shugaban kasa ya tarbi Sharif Muhammad Kabir Ibn Muhammad na Morocco, khalifan Sheikh Ahmed Tijani a fadar shugaban kasa a ranar Talata, 29 ga watan Nuwamba, 2016.

KU KARANTA KUMA: Yan Shi'a na zanga-zanga a majalisar dokoki

Ku tuna cewa shugaban kasa Buhari ya bar Marrakech, Morocco, bayan ya halarci taron Conference of the Parties (COP) na 22 zuwa taron United Nations Framework Convention on Climate Change (UNFCCC) wanda aka fi sani da COP-22, daga Nuwamba 14 zuwa 16.

Kalli wasu hotuna a kasa:

Sarki Mohammed VI na Morocco ya ziyarci Najeriya
Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo suna musabaha tare da Sarki Muhammed VI na Morocco
Sarki Mohammed VI na Morocco ya ziyarci Najeriya
Sarki Mohammed VI na Morocco ya ziyarci Najeriya

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng