Dangote zai gina kamfanin casar shinkafa a Kano

Dangote zai gina kamfanin casar shinkafa a Kano

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya tabbatar da cewa zai gina kamfanin casar shinkafa a Kano wanda zai rika amfani da shi wajen cashe shinkafar da ya noma a gonakinsa da ke jihohin Zamfara, Jigawa da Sokoto.

Dangote zai gina kamfanin casar shinkafa a Kano

Haka ma, Attajirin ya bayar da sanarwar cewa zai kaddamar da kamfanin yin takin zamani a shekara mai zuwa wanda shi ne mafi girma a nahiyar Afrika kuma zai rika samar da tan 2.8 milyan na takin zamani a kowace shekara.

A satin da ya gabata ne dai Gwamnatin Najeriya ta kulla yarjejenniya da kamfanin Dangote domin gina hanyar kankare mai nisan kilomita 42 daga garin Obajana zuwa Kabba a jihar Kogi.

KU KARANTA: An tura dubban sojoji Zamfara samar da tsaro

Kamfanin na Dangote zai kashe kimanin Naira biliyan 11 da rabi a aikin, amma an ba shi aikin ne a madadin biyan kudin haraji na sama da Naira biliyan biyar.

A yammacin jiya ranar Talata ne 22 da ga watan Nuwamba bangarorin biyu suka sanya hannu kan kwangilar a Abuja.

Babban sakatare a ma'aikatar ayyuka da gidaje da wutar lantarki Injiniya Magaji Abdullahi Gusau ne ya rattaba hannu a madadin gwamnatin tarayyar.

Yayin da mai bai wa shugaban kamfanin na Dangote shawara Injiniya Joseph Makoju ya sa hannu a madadin kamfanin, yana mai cewa, babban cigaba ne a tarihin Najeriya.

Kamfanin ya ce watanni 24 ne lokacin da aka amince kare kwangilar, amma ya ce ya kudiri aniyar kammala wa a cikin watanni 16.

A biyo mu a shafin mu na Tuwita @naijcomhausa

&feature=youtu.be

Asali: Legit.ng

Online view pixel