Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa babban birnin kasar Morocco, Marrakech da yammacin ranar Litinin 14 ga watan Nuwamba gabanin taron canjin yanayi (COP-22) da zai gudana a kasar.

Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

Shugaba Buhari ya samu tarba daga Wakilin shugaban kasa tare da ministan kasashen waje da hadin kai a filin tashin jirage na Mogado.

Shugaba Buhari ya samu rakiyar ministan harkokin kasashen waje Geofrey Onyeama, Ministan kula da yanayi Amina Mohamed, shugaban kwamitin kula da yanayi na majalisar wakilai Samuel Onuigbo, shugaban kwamitin kula da yanayi na majalisar dattawa Bukar Abba Ibrahim, da takwararsa Sanata Oluremi Tinubu.

Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

KU KARANTA: Lebura yayi ma matar Malam ciki

Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

Shugaba Buhari zai halarci taron ne kasancewar Najeriya na cikin jerin kasashen da suka rattafa hannu kan daftarin kawo karshen matsalolin da canjin yanayi ke yi ma duniya gaba daya a birnin Marrakech, za’a fara taron daga 14-16 ga watan Nuwamba.

Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

Shugaban zai halarci bikin bude taron, inda zai gabatar da kasida yayin babban taron tattaunawa na mahalarta. Sa’annan shugaban zai halarci taron bikin murnan zagayowar ranar Afirka wanda aka yi ma taken “tashi daga maganar fatar baki, zuwa aiki don bayar dagudunmuwa tare da tabbatar da shirin habbaka hanyoyin samar da wuta a Afirka”

Shugaba Buhari ya isa kasar Morocco (Hotuna)

Bugu da kari shugaba Buhari zai halarci taron shuwagabannin Afirka a yayin babban taron.

&feature=youtu.be

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng