Wata Amarya ta ruga a guje yayin da za a daura mata aure

Wata Amarya ta ruga a guje yayin da za a daura mata aure

- A jihar Delta Wata Amarya ta ruga a guje yayin da ske shirin daura mata aure

- Wannan Amarya ta ce ba tayi, ana tsakiyar taro

- An ga Angon ta a guje yana bin ta a baya, yana ba ta hakuri

Wata Amarya ta ruga a guje yayin da za a daura mata aure

 

 

 

A jihar Delta wani abin mamaki da al’aji ya faru a wannan makon. DailyPost ta rahoto cewa an dakatar da wani daurin aure bayan da Amarya ta sheka a guje ta bar wurin bikin. Wannan Amarya ta ce ita fa sam ta fasa yin auren.

Bayan ta ruga, can aka hangi Angon ta a baya yana gudu, domin ya shawo kan ta, ya ba ta hakuri. Wannan abu dai ya faru ne a Garin Udu da ke Jihar Delta. Mutane ne dai sun tsaya kallon sarautar Ubangiji, inda suka ga Ango ya bi kan titin Orhunworhun a guje yana neman Amarya ta dawo a daura masu aure.

Ana dai cikin tsakiyar biki, wannan Amarya ta arce a guje ta bar dakin taron, tace fau-fau ta kuma fasa auren. Sai dai har yanzu ba a san menene ya faru, ya jawo hakan ba. Amma dai wannan abu ya ba jama’a mamaki kwarai.

A wata Kasa kuwa wata mata ta haifi wani yaro mai kafafu barkatai guda hudu, yanzu haka ana ta kokarin yi wa wannan yaro aiki domin ceto ran sa. Wannan abin al’ajabi ya faru ne a Kasar Mozambique.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng