Rahama ta fara shirin fim tare da Akon

Rahama ta fara shirin fim tare da Akon

Tsohuwar jarumar Kannywood, Rahama Sadau ta fara aiki a shikin shirin ‘The America King’ tare  da shahararen mawaki, Akon da sauran jaruman fim.

A farkon wannan satin ne jarumar wacce ta fito a shirin wasa tare da darakta wanda ya amshi lambar yabo, Jeta Amata ta yada hotunan wasan da suke shiryawa a shafinta na zumunta tare da masoyanta.

Tace: “Kuna da daraja kuma baza’a iya canza kuba, idon wani ya taba fada maku akasin haka, karda ku yarda da hakan. Kawai kuyi kokari ku kasance kanku ko sau daya ne.”

Anyi shirin wasan ne a Los California ya kuma samu soyayyar jarumai irin su Enyina Nwigwe.

KU KARANTA KUMA: Anyiwa yar Buhari ba’a kamar yadda ta zama mata ta 4

Rahama ta fara shirin fim tare da Akon
Tsohuwar jarumar Kannywood, Rahama Sadau

An kori jarumar daga wasa a kamfanin Kannywood ne, bayan ta fito a cikin wani bidiyon waka tare da ClassicQ wanda aka zarge ta da rungumar mawakin.

Kungiyar masu ruwa da tsaki na MOPPAN ne suka kaddamar da takardan korar jarumar, bisa ga hujjar cewa abunda tayi ya saba ma kundun tsarin kungiyar, harma suka ce koda wani jarumin daban ya aikata irin abunda tayi, babu shakka doka zatayi aiki a kansa.

bayan dakatarwan tata ne shararen mawakin nan na kasar Amurka, Akon ya mika tayinsa gareta, inda ya gayyaceta zuwa Hollywood domin ta shiga cikin shirin wasar su.

https://youtu.be/-djNyHh_-y4

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng