Sabon Farashin Man Fetur
Dillalan man fetur a Najeriya sun alakanta karuwar tsadar fetur da rashin samun damar sayen mai kai tsaye daga matatar Dangote, sun ce a rumbuna suke saye.
Alhaji Aliko Dangote zai fadada matatarsa zuwa karfin tace mai ganga miliyan 1.4 a rana. Ya bayyana cewa zai dauki ma'aikata 'yan Najeriya wajen aikin.
Duk da samar da mai daga matatar Dangote, rahoton hukumar NMDPRA ya nuna Najeriya ta shigo da kusan lita biliyan 15 na fetur tun Agustan 2024 zuwa yanzu.
Matatar Dangote da ke Legas ta koka da cewa ta fuskanci matsaloli da dama ciki har da yunkurin cinna wuta. Jami'in matatar, Devakumar Edwin ne ya bayyana haka.
Farashin man fetur ya kai N1,000 a Jos, Gombe da wasu biranen Arewacin Najeriya da dama, direbobi sun koka kan tsadar man. 'Yan kasuwa sun fadi dalilin tsadar.
Kungiyoyin 'yan kasuwa sun ce ba su suka jawo tashin farashin mai a Najeriya ba. An zargi manyan dilolin mai da janyo tashin farashin mai a jihohin Najeriya.
Kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ya yi kari kan farashin litar man fetur. Kamfanin ya yi karin ne a gidajen man da ke a biranen Abuja da Legas.
Duk da janye yajin aikin PENGASSAN, karancin man fetur ya ƙara tsananta a Sokoto, inda farashin lita ya kai ₦970, lamarin da ya janyo tsadar sufuri da wahala.
A labarin nan, za a ji cewa Majalisar Wakilai ta bayyana damuwa a kan halin da matatun mai mallakin gwamnatin Najeriya ke ci gaba da lakume kudi, amma ba aiki.
Sabon Farashin Man Fetur
Samu kari