Kasashen Duniya
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya umurci fara tattaunawar zaman lafiya da Lebanon cikin gaggawa, ciki har da batun kwance damarar kungiyar Hezbollah.
Shugaban Faransa, Emmanuel MAcron ya yi Allah wadai da harin Isra'ila a Lebanon bayan tsagaita wuta da aka yi. Yai yi magana da Amurka da kasar Iran.
Gwamnatin kasar Rasha ta yi magana kan tsagaita wuta da aka yi tsakanin Iran da Amurka. Ta bayyana Hormuz a matsayin makamin nukiliyar kasar Iran.
Kasar Iran ta dauki zafi kan hare haren da Isra'ila ta kai Lebanon, ta bukaci Amurka ta zabi zaman lafiya ta hanyar tsagaita wuta ko yaki ta hannun Isra'ila.
Kasar Iran ta bayyana cewa za ta iya ficewa daga yarjejeniyar tsagaita wuta matukar aka bar Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare kan kasar Lebanon.
Rahotanni sun ce wani harin sama da Isra’ila ta kai a kudancin Lebanon ya yi sanadin mutuwar ‘yan mata uku ‘yan gida daya tare da jikkata wasu fararen hula.
Kasashen UAE, Kuwait, da Bahrain sun fuskanci harin makaman Iran yau Laraba, 8 ga Afrilu, 2026, sa'o'i kadan bayan sanarwar tsagaita bude wuta yau.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya tabo batun nukiliyar Iran. Donald Trump ya bayyana cewa akwai aikin hadin gwiwa da Amurka za ta yi tare da Iran.
Gwamnatin Pakistan ta godewa kasashen da ta kira yan uwa, wadanda suka bada gudummuwa wajen kawo karshen yakin Amurka/Isra'ila da kasar Musulunci ta Iran.
Kasashen Duniya
Samu kari