Wani sanannen mawaki a Tanzania yayi ma wata yarinya ciki

Wani sanannen mawaki a Tanzania yayi ma wata yarinya ciki

Sanannen mawaki a Tanzania mai suna Abdul Kiba yayi ma wata yarinya yar shekara 19 ciki da kuma saduwa da ita ba wata kariya.

Yarinyar da aka bayyana sunanta Nasra Salum, yar aji 2 ce a makarantar Isqama Islamic Academy a Oman, tace mawakin ya nemi da ta bashi sunan da take amfani da shi na dandalin sadarwa na Instagram , bayan ta aika masa,sai suka magana daga baya kuma suka hadu.

Wani sanannen mawaki a Tanzania yayi ma wata yarinya ciki
Abdul Kiba

Ta bayyana yadda abubuwan suka kasance ya fara nuna yana sona, yana yi maman dadin baki, gwaggo na ta fara nuna ta fara gajiya da abubuwan da nake, sai ta saya man tikiti na tafi Tanzania.

Yarinyar ta kara da cewa tana zaune da yar uwarta a Dar-res-salam, inda suka shirya yadda zasu hadu da Abdul, kuma sai ta tafi ta same sa a gidanshi da ke Tabata.

Tace" tana tare da shi har tsawon kwana2 kuma sun  sadu da ita ba wani abun kariya daga baya sai ya kyaleta kuma ya gogeta a duk dandalin sadarwa .

Bayan yan watanni da haduwa da Abdul, sai ta gano tana da ciki amma mawakin sai ya mutum ta haka.

Ban yadda tana da ciki ba, sai dai nasan na sadu da ita ba kariya lokacin da ta kwana2 a gida na, kawai ina ganin so take ta shafa man bakin fenti, na gogeta a duk dandalin sadarwa da naga ta fara damuna ,kuma karya take ba daliba bace, ta fada man ita yar kasuwa ce taba zaune a Oman.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng