Wasu abokai sun yanka wani mutum saboda yarinya

Wasu abokai sun yanka wani mutum saboda yarinya

A ranar Lahadi 18 ga watan Satumba, wasu abokai su uku sukan yanka wani mutum har lahira bayan da mutu ya barke a tsakaninsu akan wata yarinya dake Eku a karamar hukumar Ethiope ta yamma a jihar Delta.

Wasu abokai sun yanka wani mutum saboda yarinya

Acewar rahoton Southern City, al'amarin ya farune a wurin cin abincin da shaye-shaye na Blue Sea akusa da Abraka University, bayan da wasu matasa suka murkusheshi inda wni mai suna Ese Uku yayi musu jagora.

Haka kuma, an bayyana cewar Uku yasha jama Mathew kunne akan ya fita harkar yarinyar da yake nema.

Mai magana da yawun 'yan sandan jahar Delta, Celestine Kalu, ya tabbatar da aukuwar al'amarin, inda yace sun riga sun sami nasarar kama mutum biyu daga cikin su, wanda suka hada da suna Kevwe Edward dan shekara 21 dakuma Lucky Grant dan shekara 19.

Kai jama'a.....me zaisa ka kashe mutum saboda macce?

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng