Wani ya bayyana yadda ya kama kaninsa da matar fasto

Wani ya bayyana yadda ya kama kaninsa da matar fasto

- Wani mutum ya bayyana yadda ya shigo gida ya tarar da kaninsa na zina da matar malamin cocinsu

- Yayinda ya watsa wannan labara a shafin sada zumuntarsa, mutumin yace abin ya basa tsoro, yace ya dawo daga wajen aiki sai ya shiga cikin daki ya tarar da matar fasto da kaninshi zindir haihuwar uwarsu

Yace:

“Na ga wani abinda ban taba zato ba a rayuwata, da ranan nan, na kama matar faston mu, wacce nike ganin girmanta sosai, haihuwar uwarta tare da kani na. Iyayenmu sun je kauye sun bar mu biyu a cikin gida.

KU KARANTA:Allah ya kyauta! Wani yayi wa yar’uwar sa fyade

“Ina da digri amma ina koyarwa a wata makarantan Sakandare. Na bar gida da safe kuma in dawo da karfe 4 na yamma. Amma yau ba haka bane, saboda mun yi wani taro malamai sai muka tashi da wuri. Na shiga gida, kawai sai na gan su zindir haihuwar uwarsu.

“Abin ya bani mamaki. Nayi iwun sunan kanina. Amma na tafi mashaya yanzu saboda in natsu. Ban ma san abinda zanyi ba, ban ma gane abinda ya faru ba ko kuma yaya ya faru.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng