Soji da yan Boko Haram sunyi batakashi a Fatori

Soji da yan Boko Haram sunyi batakashi a Fatori

Yan Boko haram da dama da sojin rundunar Joint Multinational Task Force (MNJTF) sun rasa rayukansu a wata batakashi da akayi a Mallam Fatori a jihar Borno a ranan Talata, 21 ga watan Satumba.

Associated Press ta ruwaito cewa yan kungiyan Boko haram sun sanya a shafin sada zumuntarsu cewa sun kashe sojin MNJTF 40 amma ddai ba’a tabbatar da hakan ba har yanzu.

Soji da yan Boko Haram sunyi batakashi a Fatori

“Daular islama ta yankin Afrika ta kudu ta hallaka wata rundunar sojin afrika a garin Malam Fatori. Har yanzu dai hukumar sojin Najeriya bata fadi komai akan zancen ba kuma ba’a san adadin wadanda suka mutu ba.AP ta rubuta.

KU KARANTA: Boko Haram sun kai hari a Borno

Amma dai, hukumar Sojin Najeriya ta tabbatar da cewa anyi wata batakashi a wata jawabin da kakakin sojin ya bayyana, Kana Sani Kukasheka Usman a ranan laraba, 21 Satumba.

Jawabin ta tabbatar da cewa yan boko haram din sun dan bada wuya amma an kashe da dama daga cikin su a batakashin.

“A cigaba da Operation GAMA AIKI, rundunar Operation LAFIYA DOLE da MNJTF suka kwato garin Malam Fatori a jihar Barno bayan wata batakashi da akayi.

“Amma,yan ta’addan sun sami Karin karfi a boda Nijer. Shi yasa rundunar suke jin dadi. Sun kashe da dama daga cikin yan boko haram din amma daga baya suka koma, za’a cigaba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng