Ambaliyar Kogin jini a Bengladesh

Ambaliyar Kogin jini a Bengladesh

Kwanaki kadan da wani kogin jini a kasar Rasha ya ta da hankalin jama’a, sai ga shi wani kogin jini ya mamaye Dhaka babban birnin Bengladeshi

A cewar rahoton jaridar The Sun, manyan titunan Dhaka sun cika da ruwan da launinsa ya koma ja zur! Wanda kuma daga baya aka tabbatar da cewa jini ne na gaske.

Ambaliyar Kogin jini a Bengladesh

A cewar rahotanni, jinin da ya mayar da kogin ja, daga dubban dabbobin da ka aka yanka ne a bikin Sallar Layya a kasar a ‘yan kwanakin nan, an kuma kiyasta cewa na yanka dabbobi kimanin 100,000. In ji jaridar.

Ambaliyar Kogin jini a Bengladesh

An kiyasta kasar Bengladesh na da kimanin Musulmai miliyan 148 da 600,000 a shekara ta 2011, kuma a bikin na sallar Layya da ake gudanarwa sau daya a shekara ana yanka dabbobin da suka hada da Raguna da tumakai da sauransu a kasar.

Ambaliyar Kogin jini a Bengladesh

Sai dai wannan shekarar an gabatar da Sallar Layya ne a tsakiyar damina, a inda ranar Talata 13 ga watan Satumba ruwan sama ya yi ambaliyar ya mamaye lungu da sako na kasar, a inda magundanan ruwa masu jini, suka cukudu ruwan sama na ambaliyar, ya kuma kwarara zuwa titi.

Jaridar ta rawaito wata mace mai suna Attish Saha, wacce ta ke zaune a Dhaka na fadawa jaridar Guardian ta Burtaniya cewa, ganin wannan al’amari ya tayar mata da hankali matuka, domin a ruyuwarta ba ta taba ganin irin wannan al’amari ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng