Ministan Abuja zai kori Almajirai da mabarata daga Abuja

Ministan Abuja zai kori Almajirai da mabarata daga Abuja

- Ministan babban birnin tarayya Abuja ya umurci a kama duk mabaracin da aka gani a cikin birnin Abuja

- Ministan ya bada umurnin ayi wani shirin da zai tabbatar da cewan an mayar da su jihohin su

Shugabancin babban birnin tarayya Abuja suna shirya fidda wani tsari na kama mabarata da yan yawon bagaja a cikin birnin tarayya.

Ministan Abuja zai kori Almajirai da mabarata daga Abuja

Ministan FCT ,Muhammadu Bello ya bayyana hakan ne a ziyarar da ya kai cibiyar sauya mutane da koyon aikin hannu watau Vocational and Rehabilitation Centre da ke Kuchiko ,Karamar hukumar Bwari a Abuja, yace za’a damke duka mabarata kuma a kawo su cibiyar.

Bello yace, za’ayi wani shirin yanar gizo ga FCTA wanda zai basu ikon samun sunaye da wasu abubuwa masu muhmmancin mabaratan domin mayar da su jihohin su.

KU KARANTA:Buhari zai fitar da Najeriya daga kangi da take ciki-Masari

Ministan kuma ya bada umurnin cewa sakatariyan cigaban jama’a na FCT su tabbatar da cewa an sanya sunayen wandanda aka kama a cikin shirin yanar gizo domin samun su. Kana, hukumar kula da yanayin cikin birnin Abuja watau Abuja Environmental Protection Board (AEPB) da kuma FCT Task Team on Environment sai sun daukin sunayen duka mabaratan kafin a kai su cibiyar inda jami’an social development zasu amshe su kuma kuma su mika su ga cibiyar.

Bello kuma ya bada umurnin cewa cibiyar ta fara shirin mayar da su jihohinda suka zo bisa ga dokokin ko wani Jiha inda kowani jiha zasu karbi jama’ansu

Shugaban cibiyar, Bala Tsoho ya fada ma ministan cewa ba da dadewa aka kawo mabarata da nakassasu 145 cibiyar ba. Yace kiwon lafiya da koshin lafiya mabarata da nakassasun ya inganta daga zuwan ministan.

Amma, yan najeriya da dama sun roki shugaba buhari cewa yayi murabus saboda mawuyacin halin da yan najeriya ke ciki a gwamnatinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng