Muhimman labarun ranan talata

Muhimman labarun ranan talata

Jaridar Legit.ng ta tattaro mana muhimman labarun da sukayi kanin labarai a ranan Talata, 13 ga watan Satumba.

1.Yan bindigan Neja Delta sun sake kai hari, sunyi barazana cigaba da kai wa

Muhimman labarun ranan talata

Wasu yan bindigan neja delta sun kai hari wani kafan mann NPDC da ke Afiesere-Iwhrenene a jihar delta. Kungiyar The Niger Delta Greenland Justice Mandate ne suka dau alhakin kai harin da aka kai misalign karfe 1 na dare a rana litinin.

2.Father Mbaka yay a sake fadin wata Magana akan gwamnatin shugaba Buhari

Muhimman labarun ranan talata
Father Mbaka

Mbaka yace Buhari na aiki da wadanda suke son ganin karshen shi

Shugaban Adoration Ministry, Rev Fr Ejike Mbaka, yace shugaba muhammadu buhari yana aiki da wasu mutane wadanda basu  son ganin ya ci nasara.

3.Dalilin da yasa zan ki aiki a gwamnatin buhari idan aka nemeni inyi - Okonjo-Iweala

Muhimman labarun ranan talata

Tsohuwar ministan kudi, Okonjo-Iweala tace baza tayi aiki a gwamnatin buhari ba ko da shugaba buhari ya neme ta da tayi aiki a gwamnatinsa.

4.Goodluck Jonathan ya kaima Babangida da Abdulslam ziyara

Muhimman labarun ranan talata

Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kaima tsaffin shugabannin kasa 2 ziyara a jihar Neja a ranan talata ,13 ga watan Satumba.

5.Wani yayi mumunan martani ga yarinyar Buhari

Muhimman labarun ranan talata

Kwanakin baya ne ‘yar autar shugaban kasa,Muhammadu Buhari ,Zahra, ta ke tambayen yan najeriya matsalolinsu ta shafin sad zumunta ta twita  la’alla zata iya taimaka musu ,amma wani yayi mata mumunan martani.

6.Sojin ka na tsoron mutuwa,sai nutse wa suke cikin ruwa – Avengers ga Buhari

Muhimman labarun ranan talata

Yan kungiyan Niger Delta Avengers (NDA), suna dariya ga shugaban kasa muhammadu buhari cewa sojin shin a ta mutuwa a horon  “Crocodile Smile.”

7.Rundunar Sojin Najeriya sun kwace rafukan Neja Delta

Muhimman labarun ranan talata

Rundunar sojin najeriya sun saki bidiyo da ke nuna yadda rundunar ke horo a ‘operation crocodile smile’. Jaridar vanguard ta bada rahoto.

8.Ezekwesili ta musanta kushe Shugaba Buhari akan tattalin arziki

Muhimman labarun ranan talata
Oby Ezekwesili

Tsohuwar ministan Ilimi, Oby Ezekwesili, ta musanta rahotannin da ke cewa ta daura laifin durkushewar tattalin arzikin kasa kan shugaba Muhammadu Buhari.

9.‘ku manta da Biafra, nayi yaki ne domin hadin kan Najeriya

Muhimman labarun ranan talata
Buahari

Shugaban kasa Muhammau Buhari yayi kira ga matasan najeriya da suyi iyakan kokarinsu domin dawo da karfin najeriya ta hanyar neman ilimi,kishin kasa da kuma abubuwan da zasu kawo hadin kai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng