Sojan daya ya shirya mutuwa

Sojan daya ya shirya mutuwa

Sojan daya shirya mutuwa ma Najeriya

Wani jami’in rundunar sojan Najeriya dake yaki da yan kungiyar Boko haram a arewa maso gabashin kasarnan mai suna Sabo Habu ya bayyana yanayin aikin soja a shafinsa na Facebook.

Sojan daya ya shirya mutuwa

Ya ce wanda zan yi alfahari idan na mutu yayin yima kasa ta hidima, ba zan taba yin da na sanin mutuwa yayin kare kasata ba. idan janar zai shiga ruwa, ni wanene toh? Allah ya albarkanci rundunar sojan kasa, ina alfahari da kasancewa daya daga cikin mayakan rundunar sojan, Allah yayi ma Najeriya albarka.

Sojan daya ya shirya mutuwa
Habu Sabo

Sojojin dake yaki da mayakan Bokoharam da tsagerun Neja Delta suna fuskantar hadarurruka da dama yayin gudanar da ayyukansu.

KU KARANTA: Sojoji sun kashe Yan Boko Haram, sun kwace makamai

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya baiwa bangaren tsaro muhimmanci sosai. An zabi Buhari a matsayin shugaban kasa ne sakamakoon alkawarin da yayi wajen dawo da zaman lafiya a yankin arewa maso gabas wanda rigimar Bokoharam ta dabaibaye.

Sojan daya ya shirya mutuwa
Sojan daya ya shirya mutuwa

Gwamnatin shugaba Buhari ta samu nasara wajen karya lagon yan Bokoharam, amma har yanzu ba’a gama yakar su ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng