Buhari ya yaba ma Zuckerberg

Buhari ya yaba ma Zuckerberg

-Shugaba Buhari ya yaba da saukin halin attajiri Zuckerberg

-Buhari ya gana da attajirin a fadar shugaban kasa a cikin sirri

-Hadimin shugaban ya bayyana sakamakon ganarwa

Buhari ya yaba ma Zuckerberg

Shugaba Buhari ya yaba da saukin halin attajiri mai dandalin Facebook, duk da cewa shi ne na bakwai a jerin masu kudin duk duniya.

A bayanin da Babban mai ba shugaban kasa shawara a kan kafafen yada labarai, Femi Adesina ya lika a shafinsa na sada zumunta da muhawara na Facebook, inda ya ke bayyana abubuwan da aka tattauna a yayin ganawar, ya rawaito cewa, shugaba Buhari ya ce, halayyar matashin attajirin abin koyi ce ga ‘yan kasar.

A cewar sanarwar, shugaba Buhari ya kuma godewa shugaban Kamfanin Facebook din da samun lokacin da ya zo Najeriya, har kuma ya gana da matasan kasar, a inda suka yi musayar ra’ayi kan fasahar sadarwa mai karfafa gwiwa.

Shugaba Buhari ya kuma kara da cewa, “a al’adarmu a nan kasar, ba mu saba ganin manyan mutane attajirai kamar ka ba a cikin karamar shiga, tare da fita gudu har da share gumi a kan titi, a nan sai dai ka gansu a cikin motoci masu raba…”

KU KARANTA KUMA: Tauraron dan Adam da zai kawo cigaba Afrika ya samu matsala

A nasa jawabinsa Mark Zuckerberg ya ce, 'yan Najeriya sun burge shi da irin kwazonsu, da kokari, da kuma hazaka, musamman wadanda ya gani inda ake koyon fasahar zamani a unguwar Yaba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng