An kashe abokin Gwamna Mimiko

An kashe abokin Gwamna Mimiko

An kashe tsohon shugaban rikon jam’iyar PDP na jihar Ondo Niyi Pirisola wanda kuma amini ne ga gwamnan jihar Ondo Mimiko.

 

An kashe abokin Gwamna Mimiko
Niyi Pirisola

Lamarin ya afku ne da safiyar ranar Juma’a 2 ga watan agusta, kamar yadda wani dan unguwar ya shaida ma Legit.ng, yace mamacin na kan hanyarsa ne ta dawo daga coci inda ya kwana yana ibada lokacin da aka sassare shi da adda a kofar gidansa dake Ilutitun Osoro.

Tuni an wuce da gawarsa babban asibitin karamar hukumar Okitipupa. An haife Niyi a ranar 3 ga watan janairu 1959.

Wani sanannen mawaki a jihar Ondo ya koka da kisan Niyi, inda yace “yanzu yin garkuwa da mutane ya zama ruwan dare, yau kuma abin ya koma kisan kai. Don haka dole ne mu dinga sa ido, naji zafin mutuwar Niyi Pirisola”

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng