Mai facebook yaci abincin gargajiya

Mai facebook yaci abincin gargajiya

Mamalakkin kamfanin sadarwa ta facebook kuma na 7 cikin jerin masu kudin duniya Mark Zuckerberg ya sauka kasar Kenya don ganawa da kananan yan kasuwa.

 

Mai facebook yaci abincin gargajiya

 

Saukarsa kasan keda wuya aka hange shi yana cin abinci irin na kasar tare da abokinsa Joseph Mucheru sakataren watsa labarai na kasar, Zuckerberg yaci tuwon Ugali da kifi.

 

Mai facebook yaci abincin gargajiya

 

A jiya 1 ga watan satumba ne Zuckerberg ya sauka kasar Kenya inda ya fara kai ziyara kamfanin sarrafa na’ura mai kwakwalwa iHub.

Zuckerberg ya bayyana ganawarsa da Joseph Mucheru ta shafinsa na facebook yana cewa “na ci abincin rana tare da Joseph Mucheru sakataren watsa labarai na Kenya, mun tattauna batun samar da yanar gizo a kasar Kenya. Mun ci abinci a gidan cin abinci na MAMA OLIECH, daya daga cikin abin da nafi so idan nayi tafiya shi ne in ci abincin kasar, naji dadin tuwon Ugali tare da katon kifin.”

Mai facebook yaci abincin gargajiya

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng