Majalisan dattawa na alanta neman ma’aikata

Majalisan dattawa na alanta neman ma’aikata

- Majalisan dattawan Najeriya ta alanta talar neman ma’aikatan bidiyo guda biyu domin gidan talabijin din da ta ke shirin budewa

- Majalisan dattawa ta bayyana hakan ne ta kafar sada zumuntar ta ta Twitter

- Za’a fara nema ne daga ranar 5 ga watan Satumba

Majalisan dattawa na alanta neman ma’aikata

Suka ce: “Muna neman editocin bidiyo guda biyu domin aiki a gidan talabijin majalisa. Idan kana da bukata? Zamu fara dauka ranar 5 ga watan Satumba.

KU KARANTA: Shugaba Buhari ya amince a ciwo bashi daga kasashen waje

Amma, shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume ya bayyana cewa majalisar fa bata da kudi a yanzu. Ya fadi hakan ne a ranar talata,24 ga watan agusta. Ndume yace majalisar tarayyan na fuskanta matsala wajen sufurin kudi. Yace yan majalisan basu samun Albashi a lokacin da ya kamata kuma hakan na shafan yan siyasan.

Amma yan Najeriya sun tofa albarkacin bakinsu akan neman ma’aikatan. Da dama sun nuna bacin ran su , wani yace: “menene amfanin tallatawa tunda yan uwanku zaku dauka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng