Mata sun yi zanga-zanga a tube a jihar Kaduna

Mata sun yi zanga-zanga a tube a jihar Kaduna

-Mata sun cire tufafinsu a wata zanga-zanga a Jihar Kaduna

-Masu zanga-zangar na zargin cewa Fulani makiyaya na hallaka su da kuma yi musu fyade

-Jami’an tsaro sun ce sun karfafa matakan tsaro a yankin

Mata sun yi zanga-zanga a tube a jihar Kaduna ­
Matan masu zanga-zanga sun fito ne daga yankin Kafanchan ta karamar hukumar Jama'a

Wasu mata sun gudanar da wata zanga-zanga domin nuna rashin jin dadin su a kan abin da suka ce hare-haren da Fulani makiyaya ke kaiwa a kan kauyukansu.

Matan da sun fito ne daga kauyen Ninte da ke masarautar Godogodo a yankin Kafachan da ke cikin karamar hukumar Jama’a, sun kuma yi zanga-zangar ne a ranar Talata 2 ga watan Agusta shekarar 2016, a fadar basaraken gargajiya na Godogodo kusan a tsirara.

Jaridar The Sun ta ce, wasu mata da suke fama da irin wannan matsala a sauran yankunansu, sun fito  sun marawa matan baya a zanga-zangar, a inda suke zargin cewa Fulani makiyaya sun hallaka mutane a yankin baya da yiwa matan fyade da kone gidajensu da kumka dukiyoyi

Daya daga cikin masu zanga-zangar ta yi zargin cewa, gwamnati ta yi halin ko-oho, da kuma kin daukar matakin da ya dace kan rahotannin da ake kai mata na irin barnar da makiyayan suke yi a kauyukan yankin, a cewar masu zanga-zangar, “gwamanati ta ce mu koma gona, mun amsa kira, amma ta bar mu da makiyaya dauke da makamai su na cin zarafinmu a gonakinmu da gidajenmu”.

A cewar masu zanga-zangar, wasu mazauna kauyukan yanki sun zama ’yan gudun hijira a makwabtan kayukan saboda fargaba.

Malam Iliya Ajiyah, basaraken gargajiya na yankin, ya roki matan su kwantar da hankalinsu , ya kuma kara da cewa gwamnati na kokarin shawo kan lamarin, shi ma shugaban riko na karamar hukumar, Dakta Bege Katukah ya ce an tsaurara matakan tsaro a yankin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng