Ku bar Mata Musulmi su sanya Hijabi - Fafaroma

Ku bar Mata Musulmi su sanya Hijabi - Fafaroma

Fafaroma Farncis, shugaban Kiristoci mabiya darikar Katolika na duniya, yayi kira ga mahukunta na kasar Faransa dasu bar mata Musulmi su sanya Hijabi kamar yadda Mata Kirista ke sanya Kuross da abubuwan da suka ga dama.

Ku bar Mata Musulmi su sanya Hijabi - Fafaroma

Fafaroma ya bayyana wannan ne bayan takunkumin da kasar ta sanya akan sanya Hijabi a cikin mutane. Wasu Bidiyoyi da suka fito kwanakin baya na nuna yadda yan sandan kasar ke musguna ma Mata musulmi idan suka fito da Hijabin su.

Fafaroma Francis ya kuma yi Allah wadai da batun gina katanka domin hana bakin haure shiga wasu kasashe kamar su Amurka. Fafaroma kuma ya soki kudin dan takarar shugabancin kasar Amurka, Donald Trump akan sanya kasar Mexico ta gina katanga domin hana mutanen kasar daga shigowa kasar Amurka din idan yayi nasarar lashe zaben.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng