Liverpool sun kammala siyayyar su ta 6

Liverpool sun kammala siyayyar su ta 6

Wata kafar labarai ta kungiyar Liverpool sun sanar da cewa dan kasar Netherlands din nan wanda kuma yake buga wasa a kungiyar Newcastle watau Georgino Wijnaldum zai koma kungiyar bayan an kammala masa gwaje-gwajen lafiyar sa.

Liverpool sun kammala siyayyar su ta 6

Kafar ta labarai ta kuma ce dan wasan zai bi sauran tawagar sa ta Liverpool a can kasar Amuruka da zarar an kammala gwaje-gwajen. An dai kiyasta dan wasan zai koma Liverpool din ne a kan kudi £23m. Shi dai dan wasan ya zura kwallaye 11 a gasar firimiyar da ta gabata a tsohon kulob din sa kafin daga bisani su fada gurbin gajiyayyu.

Indai har ta tabbata to hakan zai maida shi cikon siyayya ta 6 da Liverpool din tayi kuma na biyu wajen tsada bayan Sadio Mane wanda aka sayo £30m daga Southampton. Kungiyar ta Liverpool dai tuni ta kammala siyen Mane, Joel Matip, Marko Grujic, Loris Karius da kuma Ragnar Klavan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng