Belgium ta tsallake zuwa Zagayen na biyu

Belgium ta tsallake zuwa Zagayen na biyu

Belgium da Jamani sun tsallaka zuwa zagaye na biyu a Gasar cin kofin Kwallon Nahiyar Turai

Belgium ta tsallake zuwa Zagayen na biyu
Yan wasan Belgium

Belgium ta kafa tarihin zura Kwallaye mafi yawa a gasar cin kofin nahiyar Turai na bana 2016, za su hadu da Wales a zagaye na gaba wato ‘Quarter final’. ita ma kasar Jamani ta lallasa Abokiyar karawanta ne ci 3-0. Belgium dai ta baiwa Abokiyar karawarta Hungary ne mamaki a yayin da ta yi bijibiji da ita, kuma ta fitar da ita daga gasar, wanda haka ya sa zata hadu da Wales a zagaye na biyu.

Dan wasan kasar Belgium Toby Alderweireld da ke taka leda a kulob din Tottenham dake Ingila ne ya fara bude was da cin kwallo, daga nan sai Michy Batshuayi, Eden Hazard da kuma Yannic Carrasco suka zura kwallaye a bayan an dawo hutun rabin lokaci. Haka yasa wasa ya kare a matsayin Belgium 4, Hungary 0.

Yanzu dai ta tabbata Belgium zasu hadu da Wales a fagen fafatawa don nuna kwanji tsakanin kasashen biyu. Idan ba’a manta ba, kasar Wales ta taba lallasa kasar Belgium a zagayen wasannin fidda gwani da aka buga domin cancantar zuwa gasar da ake bugawa a yanzu, duk ko da tarin sanannun yan wasanta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng