Sabon shugaban OPEC Barkindo ya ziyarci Buhari

Sabon shugaban OPEC Barkindo ya ziyarci Buhari

Dakta Barkindo ya kai wa shugaba Buhari ziyara a Abuja

Buhari ya karbi sabon shugaban kungiyar tare da karamin ministan mai Ibe Kachiku

Shugaba Muhammdu Buhari ya karbi bakuncin shugaban kungiyar kasashe masu arzikin man fetur OPEC, Dakta Mohammed Sunusi Barkindo, a fadar gwamnatin tarayya da ke Abuja.

Sabon shugaban OPEC Barkindo ya ziyarci Buhari
Shugaba Buhari tare da Barkindo, sabon shugaban OPEC

Dakta Barkindo wanda ya je fadar ta Aso Rock tare da karamin ministan mai Dakta Ibe Kachiku, shugaba Buhari ya tarbe su a ofishinsa da ke fadar a ranar Talata 21 ga watan Yuni.

Sabon shugaban OPEC Barkindo ya ziyarci Buhari
Barkindo da Ministan Mai Kachiku a ofishin shugaba Buhari a yayin ziyarar

Dakta Barkindo wanda a da, shi ne shugaban gungun kamfanin mai na Najeriya NNPC, an sanar da nadinsa ne a sabon mukamin shugaban OPEC a babban taron kungiyar karo na 169, a Vienna kasar Austria, a ranar Alhamis 2 ga watan Yuni.

Sabon shugaban OPEC Barkindo ya ziyarci Buhari
Manyan bakin a ofishin shugaban kasa a yayin ziyarar

Gwamnatin tarayya ta ce ta mika sunan Barkindo ga kungiyar, domin nada shi mukamin, ta na mai bayyana kwarewarsa a kan aiki, da kuma zurfin iliminsa. Tsohuwar minsitan mai Diezani Alison Madueke ce mace ta farko da ta taba rike mukamin a tarihin kungiyar. An kuma nada ta ne a babban taron kungiyar karo na 166 a Vienna, a watan Nuwamba 2014.

Shi ma karamin Minstan mai Dakta Ibe Kachiku ya taba rike mukamin na wani gajeren lokacin a matsayin riko bayan sauke Diezani a farkon mulkin Buhari.

 

 

 

 

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng