Yarima gwarzon Shari’a ya aske Gemu

Yarima gwarzon Shari’a ya aske Gemu

- Tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma Sanata a yanzu ya canza kamanni

- Ko kun tuna gwarzon shari’a wanda kuma ya shiga bakin duniya a sakamakon auren wata ‘yar shekara 13 ‘ya kasar Masar a ‘yan shekarun baya?

- Tsohon gwamnan jihar Zamfara Ahmed Yarima ya fita daga jerin Ustazai masu ajiye gemu.

Yarima gwarzon Shari’a ya aske Gemu
Yariman Bakura a Yanzu

Yeriman Bakura wanda ya yi suna da soma kaddamar da shari’ar Musulunci a jihar Zamfara a lokacin da ya ke gwamna, shi ne kuma wanda ya sake shiga kace-na-kace a sakamakon auren wata ‘yar Misira ‘yar shekara 13 a ‘yan shekarun bayan a lokacin yana Sanata.

Yanzu ma ya sake shiga wani kace-nacen a sakamakon aske gemu da sa kwat.

KU LURA: Za aka iya samun labara tsegunguma a manhajar Naij

An dai san Sanatan da kasancewa kullum a cikin shigar babbar riga da hula da kuma tumbujejen gemu da saje, amma a yanzu Sanatan ya canza shiga.

Kamar yadda aka ga tsohon gwamnan a Abuja a ‘yan kwanakin nan, gwarzon na shari’a ya koma shigar kwat da turoza da laktayin, ya kuma aske gemu da sajen da aka san cewa sunna ce, kuma alama ta dattijantaka a al’adar Hausawa.

Wannan sabuwar shiga ta Yariman Bakura ta janyo kace-nace musamman a dandalin sada zumunta da muhawara na intanet. Shin kuma ko menene ra’ayinku dangane da wannan birgiman hankakan?

 

 

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng