Manyan labarai guda 10 wadanda sukayi fice a ranar Laraba

Manyan labarai guda 10 wadanda sukayi fice a ranar Laraba

Legit.ng tattara maku manyan labarai guda 10 wadanda sukayi fice a ranar Laraba 25 ga watan Mayu na 2016. Ku duba domin ku samu wadannan manyan labaran.

Manyan labarai guda 10 wadanda sukayi fice a ranar Laraba
Sanata Bukol Saraki a kotun CCT

1. Sanata Bukola Saraki ya koma kotun CCT

Shugaban majalisar Dattawan Najeriya, Bukola Saraki ya sake komawa kotun CCT a cigaba da shari'ar shi da ake gudanarwa.

2. Boko Haram ta kara kai hari akan garuruwa 5 a jihar Borno

Boko Haram ta kai hari akan kyayuka 5 wadanda suke kusa da Ladin Buta kusa da Khaddamari dake a karamar hukumar Jere a jihar Borno.

3. An kama wasu da ake zargin cewa su suka kai hari a Nimbo

An kama wasu mutane da ake zargin cewa su suka kai hari a garin Nimbo dake a karamar hukumar Uzo-Uwanni a jihar Enugu.

4. Tsohon gwamnan Kaduna ya mutu

A jiya ne Manjo Janar Abubakar Tanko Ayuba ya rasu da shekaru 70. An taba bashi Kambi Nelson Mandela na kakkyawan shugabanci.

5. Gwamnatin tayi nadin shugabannin wasu manyan hukumomi

A jiya ne Gwamnatin Najeriya ta nada sabbin shugabanin manyan hukumomin dake karkashin ma'aikatar labarai. Hukumomin sune NTA, da sauran su.

6. Gwamnatin Tarayya ta bada hutu a ranar ga watan Mayu

Gwamnatin Najeriya ta bada hutu a ranar 30 ga watan Mayu domin a gudanar da hutun ranar Damakaradiyya.

7. An kama wata mata na kokarin yima wani Fasto Sherri

Wata mata yar shekara 30 mai suna Joy Ogundare zata gurfana a gaban Babbar Kotun Kano akan kokarin yima ani Fasto Sherri.

8. Allah wadarai da karin farashin Mai - Fayose

Gwamnan jihar Ekiti yayi Allah wadai da karin farashin Mai a karkashin Gwamnatin Buhari

9. An kama wasu yan Najeriya masu karuwanci a kasar Rasha

Wasu Yan Mata da ake zargin cewa karuwai an kama su a klasar Rasha inda aka tozarta su.

10. An ga gawar Sanata Ofia Nwali

Bayan da aka tsinci gawar shi a cikin Rijiya, jami'an Yn sanda sun bayyana cewa suna gudanar da biki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng