Dalilin da yasa Buhari ya ki magana a kan harbin Lekki - Fadar shugaban kasa

Dalilin da yasa Buhari ya ki magana a kan harbin Lekki - Fadar shugaban kasa

- Fadar shugaban kasa Muhammadu Buhari ta sanar sa dalilinta na yin shiru a kan harbe-harben Lekki

- Mai bai wa shugaban kasar shawara na musamman a fannin yada labarai, Femi Adesina ya sanar da dalilin

- Ya ce zai zama tamkar riga Malam masallaci ne domin ba a kammala bincike a kan lamarin ba

Shugaban masa Muhammadu Buhari bai ce komai a man harbe-harben da aka yi wa masu zanga-zangar EndSARS a Lekki a ranar Talata ba a jawabin da yayi ga 'yan Najeriya saboda baya son yayi riga Malam masallaci.

Da yawa daga cikin 'yan Najeriya sun nuna damuwarsu a kan rashin maganar shugaban kasan ko jaje ga jama'ar da suka rasa rayukansu. Sun kwatanta hakan da ganganci da kuma rashin nuna kulawa.

KARANTA WANNAN: PDP ta dakatar da ayyukan siyasa da shirin zabe saboda #EndSARS

Dalilin da yasa Buhari ya ki magana a kan harbin Lekki - Fadar shugaban kasa
Dalilin da yasa Buhari ya ki magana a kan harbin Lekki - Fadar shugaban kasa - @NGRPresident
Asali: Twitter

Amma kuma, mai bai wa shugaban kasar shawara na musamman a fannin yada labarai, Femi Adesina, wanda ya bayyana a shirin siyasarmu a yau a gidan talabijin na Channels, ya ce shugaban kasan bai samu cewa komai a kan harbin ba saboda ba a kammala bincike a kai ba.

KARANTA WANNAN: Jami'an tsaro na kallo mutane suka sace tallafin COVID-19 a Kwara

Ya ce: "Hedkwatar tsaro ta fitar da takarda inda tace tana bincikar lamarin. Gwamnan jihar Legas ya kafa kwamitin bincike a kan abinda ya faru.

"Toh don haka shugaban kasan bashi da ta cewa saboda zai zama tamkar riga Malam masallaci ne a kan binciken da ake yi. Bayan binciken ne zai yanke hukuncin magana a kai."

A wani labarin, Jam'iyyar PDP ta ce ta dakatar da duk wasu ayyukan siyasa a yanzu.

Jam'iyyar ta sanar da hakan ne a wata takarda da sakataren yada labaran jam'iyyar, Kola Ologbondiyan, ya saki a ranar Juma'a a Abuja.

Ologbondiyan ya ce sun dauki wannan matakin ne don nuna alhininsu a kan kisan matasa da aka yi a Lekki Toll Gate da sauran kashe-kashe da aka yi sakamakon zanga-zangar EndSARS.

Dama da safiyar Alhamis jam'iyyar PDP ta umarci a kwantar da tutocin ta da ke kowanne ofishi a fadin kasar nan saboda lokacin nan mai cike da kalubale.

PDP ta roki INEC ta dage zabuka 15 da aka shirya yi a ranar 31 ga watan Oktoba a kasar nan.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng