EndSARS: Akwai yuwuwar mu sassauta dokar kulle a ranar Juma'a - Sanwo-Olu

EndSARS: Akwai yuwuwar mu sassauta dokar kulle a ranar Juma'a - Sanwo-Olu

- Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya sanar da lokacin da zai cire kulle a wata hira da aka yi da shi

- A cewarsa, matsawar babu kowa a tituna, zai saki kullen da yasa a ranar Juma'a, 23 ga watan Oktoba

- Ya ce da zarar al'amura sun daidaita, babu makawar sakin kullen, don a cigaba da komai kamar da

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, a ranar Alhamis, 22 ga watan Oktoba, ya bayyana ranar da zai cire kullen da yasa a jihar Legas.

A wata hira da gidan talabijin din Arise suka yi da gwamnan, ya ce za'a cigaba da shige da fice a jihar daga ranar Juma'a, 23 ga watan Oktoba.

Sanwo-Olu yace zai aiwatar da hakan matsawar rikicin ya yi kasa.

A cewarsa, "Matsawar masu zanga-zangar EndSARS suka bar tituna, zuwa gobe zan saki kullen, yadda al'amura zasu koma yadda suke."

KU KARANTA: Dole a sallami shugabannin tsaro, ka sauya salon mulki - Dattawan arewa

EndSARS: Akwai yuwuwar mu sassauta dokar kulle a ranar Juma'a - Sanwo-Olu
EndSARS: Akwai yuwuwar mu sassauta dokar kulle a ranar Juma'a - Sanwo-Olu. Hoto daga punchng.com
Asali: Twitter

KU KARANTA: Shiru magana ce, caccakata a yanar gizo ba mafita bace - Fatima Ganduje-Ajimobi

A wani labari na daban, fitaccen marubuci, Farfesa Wole Soyinka, ya yi kira ga gwamnonin da suka sa kulle a jihohin su saboda rikicin SARS da su yi gaggawar dakatar da sojojin da gwamnatin tarayya ta tura jihohin.

Ya rubuta wannan sakon ne a ranar Laraba a gidansa da ke Abeokuta, jihar Ogun, yayi magana cikin matsananciyar damuwa, inda yace sojojin dake Lekki toll gate a Legas suna kashe masu zanga-zanga a ranar Talata da daddare bayan saka kullen awanni 24 da gwamnan jihar, Babajide Sanwo-Olu yayi.

Marubucin yace, "Ga gwamnonin da ya shafa, akwai abinda yafi dacewa kuyi: Ina bukatar ku cire wadannan sojojin. Kuyi gaggawar hada taro don yin gyara aka al'amarinnan."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng