EndSARS: Buhari ya gana da ministan tsaro tare da shugaban tsaro

EndSARS: Buhari ya gana da ministan tsaro tare da shugaban tsaro

- Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya shiga ganawar sirri da ministan tsaro tare da shugaban tsaro

- Duk da ba a san abinda suka tattauna ba a ganawar, ana zaton tarzomar da ke karuwa a fadin kasar nan ce

- Duk da kokarin gwamnati na ganin ta cimma bukatun masu tarzomar, a koda yaushe rikicin na cigaba da karuwa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kammala taron sirri da minsitan tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi da shugaban ma'aikatan tsaro, Janar Gabriel Olonisakin a fadarsa, The Nation ta wallafa.

Duk da har yanzu babu bayani a kan abinda suka tattauna yayin taron, a lokacin rubuta wannan rahoton an gano cewa sun tattauna ne a kan yadda za a shawo kan tarzomar EndSARS da ke ta'azzara.

Idan za mu tuna, a cikin kwanaki biyu da suka gabata an ga yadda zanga-zangar lumanar ta koma zubda jini a sassa daban-daban na kasar nan inda jama'a da kadarori suka salwanta.

Duk da gwamnatoci a kowanne mataki sun tashi tsaye wurin tabbatar da bukatu biyar da masu zanga-zangar suka mika, lamarin ya ki ci balle cinyewa kuma hakan yana kawo sabbin bukatu a kowacce rana.

KU KARANTA: Ga lokacin da ASUU za ta janye yajin aiki - Kungiyar da FG sun cimma matsaya

EndSARS: Buhari ya gana da ministan tsaro tare da shugabannin tsaro
EndSARS: Buhari ya gana da ministan tsaro tare da shugabannin tsaro. Hoto daga @TheNation
Asali: Twitter

KU KARANTA: Bidiyon ragargazar 'yan Boko Haram da sojin sama suka yi a maboyarsu a Borno

A wani labari na daban, Shugaban kasa Muhammadu Buhari yace matasa su na da hakkin yin zanga-zanga don sanar da shugabanninsu matsalarsu, Vanguard ta ruwaito.

Ya ce yakamata a ba wa matasa damar bayyanar da damuwarsu da hakkinsu ga gwamnati, amma kada su bar 'yan ta'adda da bata-gari su shiga harkar.

Ministan matasa da wasanni, Sunday Dare, ya sanar da hakan bayan taron da yayi da shugaban kasa a fadarsa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng