EndSARS: Babu jinin dan Najeriya da ya cancanci zuba - Goodluck Jonathan

EndSARS: Babu jinin dan Najeriya da ya cancanci zuba - Goodluck Jonathan

- Tsohon shugaban kasan Najeriya, Dr. Goodluck Jonathan, Yace bai dace a zubar da jinin wani ba akan zanga-zangar rushe SARS ba

- Yace 'yan Najeriya na yin wannan zanga-zangar lumanar ne don ci gaban Najeriya don haka bai dace ace an cutar da wani ba

- Ya kuma kara rokon 'yan Najeriya akan kowa ya kwantar da hankalinsa musamman a irin wannan lokacin na tsanani

Tsohon shugaban kasan Najeriya, Dr. Goodluck Jonathan, yace bai dace a zubar da jinin wani dan Najeriya ba a saboda zanga-zangar lumana akan SARS.

Yace ya lura zanga-zangar da suke yi don ci gaban kasa suke yi, jaridar Vanguard ta wallafa hakan.

Tsohon shugaban kasan, yayi maganar ne a shafinsa na kafar sada zumuntar zamani ta Twitter, inda yake rokon tabbatar da adalci ga lamarin.

Kamar yadda Goodluck Jonathan ya wallafa, "Babu jinin dan Najeriyan da ya dace a zubar ta dalilin neman cigaban Kasarmu.

"Zamu iya yin tunani daban-daban akan al'amuran da suka shafi kasa, amma babu kuskure, kowanne dan Najeriya na son cigaban ta."

"Ina son kowa ya kwantar da hankalinsa musamman a wannan lokacin na tsanani," a cewar Goodluck.

KU KARANTA: Magidanci ya saka wa bishiyarsa raga domin hana makwabta amfana da ita

EndSARS: Babu jinin dan Najeriya da ya cancanci zuba - Goodluck Jonathan
EndSARS: Babu jinin dan Najeriya da ya cancanci zuba - Goodluck Jonathan. Hoto daga @Vanguard
Asali: UGC

KU KARANTA: Abubuwa 6 da ya kamata a sani game da sabuwar rundunar SWAT ta 'yan sanda

A wani labari na daban, fadar shugaban kasa tace an sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari akan zanga-zangar da matasa ke yi saboda kashe-kashen da jami'an SARS ke yi.

Bashir Ahmad, hadimin shugaban kasa akan harkokin watsa labarai ya sanar da hakan a ranar Juma'a, 9 ga watan Oktoba, matasa na tsaka da zanga-zanga akan kisan wulakanci da 'yan sanda ke yi.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng