Rufe sashin tsokaci a Twitter: 'Yan Najeriya sun caccaki Shugaba Buhari

Rufe sashin tsokaci a Twitter: 'Yan Najeriya sun caccaki Shugaba Buhari

- Ma'abota amfani da kafar sada zumuntar zamani ta Twitter sun caccaki shugaba Buhari tare fadarsa

- Fadar shugaban kasan ta wallafa yadda ta kaddamar da layin dogo wanda ya fara daga Itakpe har zuwa Warri

- Rufe sashin tsokacin ya janyo wa fadar shugaban kasa cece-kuce domin wasu sun zargesu da hana jama'a fadin ra'ayinsu

'Yan Najeriya sun caccaki shugaban kasa Muhammadu Buhari da fadarsa sakamakon rufe sashin tsokaci na shafinsu a Twitter da suka yi.

Shugaban kasar ya bayyana cewa ya kaddamar da titin jirgin kasa daga Itakpe zuwa Warri.

Amma kuma sai aka kulle sashin tsokacin a wallafar, lamarin da yasa 'yan Najeriya suka kasa fadin albarkacin bakinsu a kan al'amarin.

Yayin da wasu suka kushe wannan hukuncin na rufe sashin tsokacin, sauran sun ce ta yuwu shugaban kasan ya gaji da shakiyancin 'yan Najeriya ne.

KU KARANTA: 'Yan sanda sun damke 'yan fashi 7 da suka addabi jihar Adamawa (Hotuna)

Rufe sashin tsokaci a Twitter: 'Yan Najeriya sun caccaki Shugaba Buhari
Rufe sashin tsokaci a Twitter: 'Yan Najeriya sun caccaki Shugaba Buhari
Source: Twitter

KU KARANTA: Nigeria @ 60: Buhari zai yi jawabi ga 'yan Najeriya daga Eagle Square

A wani labari na daban, a ranar Alhamis, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mawuyacin hali a fannin tattalin arziki.

Ya ce hakan kuwa daidai yake da kowacce kasa domin kuwa dukkan duniya ne ake cikin wannan halin.

Buhari ya sanar da hakan ne a jawabinsa ga 'yan Najeriya a ranar da kasar ta cika shekaru 60 da samun 'yancin kai.

Shugaban kasar ya kara da amincewa da cewa, kasar na fuskantar matsalolin tsaro daban-daban a sassan kasar.

Ya ce, "A yau na tabbatar da cewa Najeriya tana cikin mawuyacin hali na tattalin azriki kuma hakan ce ta kasance ga kowacce kasa a fadin duniya. Muna fuskantar kalubalen tsaro a sassa daban-daban na kasar nan."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng