Da duminsa: Rikici ya barke a jam'iyyar PDP reshen Ekiti, jam'iyyar ta dare gida 2

Da duminsa: Rikici ya barke a jam'iyyar PDP reshen Ekiti, jam'iyyar ta dare gida 2

- Rikicin da ya mamaye jam'iyyar PDP reshen jihar Ekiti ya kara tsamari, jam'iyyar ta dare gida biyu a ranar Asabar

- Rashin jituwar da ta shiga tsakanin Sanata Biodun Olujimi da Mr Ayo Fayose ta zama sanadin rabewar jam'iyyar

- Hon. Bisi Kolawole ya zama shugaban jam'iyyar daga bangaren Fayose, amma a bangaren Olujimi, Hon. Kehinde Odebunmi ne shugaban jam'iyyar

Rikicin da ya mamaye jam'iyyar PDP reshen jihar Ekiti ya kara tsamari a ranar Asabar, sakamakon rabewar jam'iyyar gida biyu, inda kowanne bangare ya zabi shuwagabannin sa.

Jam'iyyar PDP ta kasance cikin rabuwar kai a 'yan kwanakin nan, sakamakon rashin jituwar da ta shiga tsakanin Sanata Biodun Olujimi da Mr Ayo Fayose.

Sanata Biodun dai ita ce mai wakiltar mazabar Ekiti ta Kudu a majalisar dattijai, yayin da Mr Ayo shine tsohon gwamnan jihar, lamarin da ya jawo rabuwar kai a jam'iyyar.

Rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa ne ya tilasta kwamitin shugabancin jam'iyyar na kasa (NWC) a kafa kwamitin rikon kwarya na mutane bakwai da zai jagoranci jam'iyyar a jihar.

Kwamitin rikon kwaryar na karkashin shugabancin tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattijai, Sanata Hosea Agboola.

KARANTA WANNAN: Bayan shekara daya: Tashar jiragen sama ta Enugu za ta dawo bakin aiki

Da duminsa: Rikici ya barke a jam'iyyar PDP reshen Ekiti, jam'iyyar ta dare gida 2
Da duminsa: Rikici ya barke a jam'iyyar PDP reshen Ekiti, jam'iyyar ta dare gida 2
Asali: Twitter

A taron zaben jam'iyyar da aka gudanar a ranar Asabar, tsohon kwamishin muhalli na jihar, Hon. Bisi Kolawole ya samu nasarar zama shugaban jam'iyyar daga inuwar Fayose.

Sai dai, a bangaren Olujimi, itama ta fitar da tsohon dan majalisar wakilai, Hon. Kehinde Odebunmi a matsayin shugaban jam'iyyar.

Tawagar Fayose ta gudanar da zabenta a kan idanun tsohon gwamnan jihar, Segun Oni, a ginin baki na Petim, da ke a gidan baki na Lotus, babban birnin jihar.

Fayose ya gargadi mambon jam'iyyar da su kauracewa rashin da'a da biirewa umurnin jam'iyya, yana mai cewa an zalunci PDP a zaben 2018, amma 2022 na nan zuwa don daukar fansa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng