Da duminsa: Yan majalisa 17 na jihar Edo sun tsige kakakin majalisasu

Da duminsa: Yan majalisa 17 na jihar Edo sun tsige kakakin majalisasu

Yan majalisu 17 na majalisar dokokin jihar Edo, da suka hada da mambobi 14 da a baya aka bayyana kujerarsu a matsayin wofi, sun yi ikirarin cewa sun tsige kakakin majalisar jihar, Francis Okiye, da mataimakinsa, Roland Asoro.

Sun yanke wannan hukuncin ne a ranar Alhamis a wani boyayyen wuri a Benin City, babban birnin jihar, awanni bayan da jami'an tsaro suka mamaye zauren majalisar.

A bangarensu, sunce sun nada Victor Edoror, mai wakiltar mazabar Esan ta tsakiya, da Emmanuel Agabje, daga mazabar Akoko-Edo II a matsayin kakakin majalisar da mataimakinsa.

A wajen taron, 'yan majalisu 14 da aka zabe su, an rantsar da su tare da sauran 'yan majalisun 3 wadanda suka yi mubayi'a ga Osagie Ize-Iyamu na jam'iyyar APC, suka ce sun tsige kakakin.

Majalisar dokokin jihar Edo ta kasance cikin rikici tun a shekarar 2019, wacce ta sake rikicewa a yanzu a yayin da ake shirye shiryen zaben gwamnan jihar.

KARANTA WANNAN: Gwamnan Bauchi ya nada hadima mai kula da harkokin zawarawa

Da duminsa: Yan majalisa 17 na jihar Edo sun tsige kakakin majalisasu
Da duminsa: Yan majalisa 17 na jihar Edo sun tsige kakakin majalisasu
Asali: Depositphotos

An zabi 'yan majalisu 24 daga mazabu 24 na jihar a babban zaben 2019. Sai dai, 10 daga cikinsu, an rantsar da su ne a ranar 17 ga watan Yulin shekarar, lamarin da ya jawo zaune-tsaye.

Biyar daga cikin 10 na 'yan majalisun an rantsar da su tare da mataimakin kakakin majalisar na wancan lokacin, Yekini Idiaye, kuma sun yi mubayi'a ga Ize Iyamu a makon da ya wuce.

Wannan lamarin ya faru ne bayan da suka zargi gwamnan jihar Godwin Obaseki da mayar da majalisar dokokin jihar ba a bakin komai ba.

Domin daukar mataki a hannunsu, a ranar Laraba, 'yan majalisun hudu cikin biyar, suka taru suka tsige Idiaye, tare da maye gurbinsa da Asoro.

Amma 'yan majalisun da ke goyon bayan Ize-Iyamu sun yi ikirarin cewa su sun tsige shi tare kakakin majalisar jihar, Okiye.

Cikakken labarin yana zuwa...

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng