Yanzu-yanzu: Dalibai sun koma makaranta a Nigeria, sun fara shirin zana jarabawa
Rahotannni sun bayyana cewa an bude makarantun sakandire, firamare da kwalejojin kimiyya a fadin Nigeria, domin ci gaban da karatu.
Sharuddan da aka gindayawa makarantun a yayin budewa sune wanke hannuwa, amfani da makarin fuska, amfani da sinadarin kashe kwayoyin cuta da gwajin zafin jiki.
Babban sharadin shine tabbatar da bata tazara a tsakanin dalibai, malamai da ma'aikata a yayin da ake gudanar da ayyukan makarantar.
KARANTA WANNAN: Bukukuwan Sallah: Yadda mata 7 suka mutu a gidan kitso
Wakilan Legit.ng sun ziyarci wasu daga cikin makarantun jihar Lagos, domin ganin yadda makarantun ke bin sharuddan da aka gindaya masu.
Gwamnatin tarayya ta baiwa makarantun damar budewa, domin ba dalibai damar zana jarabawar kammala sakandire. Hakan na zuwa bayan shafe watanni makarantun na a kulle, sakamakon barkewar annobar korona.
Ga hotunan da wakilanmu suka dauka a yayin ziyarar gani da ido a makarantun.

Asali: UGC

Asali: UGC

Asali: UGC

Asali: UGC

Asali: Original
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng