Ma'aurata sun azabtar da yaron gida kan ƙosan N100

Ma'aurata sun azabtar da yaron gida kan ƙosan N100

Jami'an tsaro na hedikwatar 'yan sanda da ke garin Orji a jihar Imo, sun cafke wasu ma'aurata; Goodluck Ogbuji da matarsa; Benita kan zargin aikata laifin cin zarafin dan Adam.

Mijin da matarsa sun shiga hannu sakamakon azabtar da Wisdom, wani yaron gidansu wanda bai wuce shekaru takwas ba a duniya kan ƙosan Naira 100.

Wasu ma'aikatan jarida biyu; Chidiebube Okeoma da Harriet Ijeomo, su ne suka yi wa ma'aurantan biyu cunen jami'an tsaro har gidansu a Unguwar Umudagu Mbieri da ke karamar hukumar Mbaitoli ta jihar.

Ana zargin magidantan biyu sun gallazawa yaron nasu azabar tsiya saboda kawai ya sayo ƙosan Naira 100 a maimakon na Naira 50.

Babban Sufeton 'Yan Sanda na Najeriya; Muhammadu Adamu
Babban Sufeton 'Yan Sanda na Najeriya; Muhammadu Adamu
Asali: Twitter

Okeoma ya ce, "Mun samu labarin cewa ma'auratan sun ci zarafin yaron gidan nasu da har suka kusa su kashe shi saboda ya sayo ƙosan Naira 100 a maimakon na Naira 50."

"Mun yi bincike ta hanyar zaurukan sada zumunta kuma muka sami adireshin gidansu."

"Jami'an 'yan sanda sun yi wa gidan dirar mikiya tun da duku-dukun ranar Alhamis, inda suka cafke azzaluman ma'auratan tare da ceto yaron gidan."

"A yanzu haka suna tsare a ofishin 'yan sanda na Orji yayin da jami'ai ke ci gaba da kula da yaron."

"Girman raunukan da suka gadar wa yaron ya nuna mafi kololuwar zalunci. Muna neman a bi masa hakkinsa."

KARANTA KUMA: Gwamnatin tarayya ta warewa 'yan siyasa kashi 10% na guraben kananan ma'aikata 774,000 da za ta dauka

"Muna son a gurfanar da ma'aurantar a gaban kuliya domin a zartar musu da hukunci kwatankwacin laifin da suka aikata."

A ofishin 'yan sandan, Uwargijiyar yaron, ta amsa laifinta da cewa sharrin Shedan ne kuma a yanzu tana cizon yatsa.

Sai dai kakakin rundunar 'yan sanda na jihar, Orlando Ikeokwu, ya ce za su yi dukkanin abinda ya dace wajen tattaro hujjojin gurfanar da ma'aratan biyu a gaban alkali.

Kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito, tun a shekarar 2019 ne Wisdom ya daina zuwa makaranta domin yi wa ma'auratan bauta.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng