Ma'aurata sun azabtar da yaron gida kan ƙosan N100

Ma'aurata sun azabtar da yaron gida kan ƙosan N100

Jami'an tsaro na hedikwatar 'yan sanda da ke garin Orji a jihar Imo, sun cafke wasu ma'aurata; Goodluck Ogbuji da matarsa; Benita kan zargin aikata laifin cin zarafin dan Adam.

Mijin da matarsa sun shiga hannu sakamakon azabtar da Wisdom, wani yaron gidansu wanda bai wuce shekaru takwas ba a duniya kan ƙosan Naira 100.

Wasu ma'aikatan jarida biyu; Chidiebube Okeoma da Harriet Ijeomo, su ne suka yi wa ma'aurantan biyu cunen jami'an tsaro har gidansu a Unguwar Umudagu Mbieri da ke karamar hukumar Mbaitoli ta jihar.

Ana zargin magidantan biyu sun gallazawa yaron nasu azabar tsiya saboda kawai ya sayo ƙosan Naira 100 a maimakon na Naira 50.

Babban Sufeton 'Yan Sanda na Najeriya; Muhammadu Adamu
Babban Sufeton 'Yan Sanda na Najeriya; Muhammadu Adamu
Asali: Twitter

Okeoma ya ce, "Mun samu labarin cewa ma'auratan sun ci zarafin yaron gidan nasu da har suka kusa su kashe shi saboda ya sayo ƙosan Naira 100 a maimakon na Naira 50."

"Mun yi bincike ta hanyar zaurukan sada zumunta kuma muka sami adireshin gidansu."

"Jami'an 'yan sanda sun yi wa gidan dirar mikiya tun da duku-dukun ranar Alhamis, inda suka cafke azzaluman ma'auratan tare da ceto yaron gidan."

"A yanzu haka suna tsare a ofishin 'yan sanda na Orji yayin da jami'ai ke ci gaba da kula da yaron."

"Girman raunukan da suka gadar wa yaron ya nuna mafi kololuwar zalunci. Muna neman a bi masa hakkinsa."

KARANTA KUMA: Gwamnatin tarayya ta warewa 'yan siyasa kashi 10% na guraben kananan ma'aikata 774,000 da za ta dauka

"Muna son a gurfanar da ma'aurantar a gaban kuliya domin a zartar musu da hukunci kwatankwacin laifin da suka aikata."

A ofishin 'yan sandan, Uwargijiyar yaron, ta amsa laifinta da cewa sharrin Shedan ne kuma a yanzu tana cizon yatsa.

Sai dai kakakin rundunar 'yan sanda na jihar, Orlando Ikeokwu, ya ce za su yi dukkanin abinda ya dace wajen tattaro hujjojin gurfanar da ma'aratan biyu a gaban alkali.

Kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito, tun a shekarar 2019 ne Wisdom ya daina zuwa makaranta domin yi wa ma'auratan bauta.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel