Da duminsa: FG ta sanar da sabuwar ranar fara WASSCE

Da duminsa: FG ta sanar da sabuwar ranar fara WASSCE

A ranar Litinin, gwamnatin tarayya ta bukaci dukkan makarantun sakandire da ke fadin kasar nan da su bude don dalibai da ke ajin karshe su kammala. Za a bude makarantun ne a ranar 4 ga watan Augusta.

An sanar da cewa, za a fara jarabawar kammala sakandire wacce hukumar shirya jarabawa ta yammacin Afrika ke shiryawa farawa a ranar 17 ga watan Augusta.

Wannan na kunshe ne a wata takarda da daraktan yada labarai da hulda da jama'a na ma'aikatar ilimi, Ben Goong ya sa hannu.

Gwamnatin tarayya (FG) ta sanar da cewa za a bude makarantun sakandire a fadin kasa domin bawa daliban da ke shekarar karshe damar zana jarrabawar kammala karatun sakandire (WASSCE).

A cikin wata sanarwa da ma'aikatar ilimi ta fitar a yau, Litinin, ta bayyana cewa za a bude makarantun ne daga ranar Talata, 4 ga watan Agusta, 2020.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Ben Bem Goong, darektan yada labarai na ma'aikatar ilimi ta kasa.

A cewar sanarwar, an yanke shawarar bude makarantun ne bayan masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi sun shafe lokaci mai tsawo suna tattaunawa a ranar Litinin.

Daliban da ke aji shidda; watau shekarar karshe, da takwarorinsu da ke aji uku ne kawai zasu koma makaranta, a cewar sanarwar.

Da duminsa: FG ta sanar da sabuwar ranar fara WASSCE
Da duminsa: FG ta sanar da sabuwar ranar fara WASSCE. Hoto daga The Punch
Asali: Twitter

KU KARANTA: Korar Sanusi II daga Kano da tsaresa: IGP ya bukaci kotu da ta yi watsi da karar

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Ben Bem Goong, darektan yada labarai na ma'aikatar ilimi ta kasa.

A cewar sanarwar, an yanke shawarar bude makarantun ne bayan masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi sun shafe lokaci mai tsawo suna tattaunawa a ranar Litinin.

Daliban da ke aji shidda; watau shekarar karshe, da takwarorinsu da ke aji uku ne kawai zasu koma makaranta, a cewar sanarwar.

"Za a bude makarantn sakandire daga ranar 4 ga watan Agusta, 2020, ga daliban ajuzuwan da zasu rubuta jarrabawar kammala makaranta. Hakan zai bawa dalibai damar yin amfani da sati biyu domin yin shirin jarrabawar WAEC, wacce za a fara ranar 17 ga watan Agusta," a cewar sanarwar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng