'Yan Fashin Daji: An tura karin ‘yan sanda 780 zuwa Zamfara

'Yan Fashin Daji: An tura karin ‘yan sanda 780 zuwa Zamfara

Hukumar jami'an tsaro ta 'yan sanda, za ta tura karin jami'anta 780 zuwa jihar Zamfara domin kara kaimi a fafutikar da ake yi na kawo karshen masu tayar da kayar baya a jihar.

Gwamnan jihar Muhammadu Bello Matawalle, shi ne ya sanar da hakan yayin zantawa da manema labarai a ranar Juma'a cikin birnin Abuja.

Kamar yadda Gwamnan ya bayyana, sufeto janar na 'yan sanda, Muhammad Adamu, shi ne ya bayar da amincewarsa a kan wannan lamari.

Yusuf Idris, Darakta Janar na sadarwa da hulda da al'umma ga gwamnan, shine ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Litinin a babban birnin Zamfara, Gusau.

Shugabannin tsaro na Najeriya
Hoto daga fadar shugaban kasa
Shugabannin tsaro na Najeriya Hoto daga fadar shugaban kasa
Asali: UGC

Mista Idris ya ce Gwamna Matawalle ya samu wannan amincewa ne a yayin da ya ziyarci babban sufeton na 'yan sanda a hedikwatar rundunar a ranar Juma'a, 3 ga watan Yuli.

Ya ce daga cikin ma'aikatan da za a turo jihar za su kunshi jami'an rundunoni daban-daban ciki har da 'yan sanda masu jiran ko ta kwana, yaki da ta'addanci da kuma rundunan 'yan sanda ta musamman.

Hadimin gwamnan ya ce sabbin jami'an da za a turo za su hada karfi da karfe tare da ragowar 'yan sandan da ke jihar wajen kawar da 'yan tsirarun masu tayar da kayar baya da suka rage a jihar.

KARANTA KUMA: Babu sauran mai dauke da kwayoyin cutar korona a Jigawa - Dr. Zakari

Ya kara da cewa, gwamnan ya yi godiya ga gwamnatin tarayya da sauran hukumomin tsaro da ke fadi-tashin kawo karshen musibar da ta addabi jihar.

Legit.ng ta kuma ruwaito cewa, rayukan mutum uku sun salwanta a wani sabon hari da 'yan bindiga suka kai wasu kauyuka a karamar hukumar Matazu ta jihar Katsina.

Yayin harin na dare da 'yan bindigar suka kai a karshen makon da ya gabata, sun kuma yi awon gaba da shugaban jam'iyyar APC na karamar hukumar, Yusha'u Dissi tare da wata mata.

Haka zalika a wannan dare, 'yan bindigar sun kai hari wasu kauyuka na karamar hukumar Batsari ta jihar kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

A kauyen Dan Alhaji, 'yan bindiga sun bude wa mutanen kauyen wuta ta harsashin bindiga kan mai uwa da wabi, inda suka kashe mutum daya.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng