Gwamnatin Tarayya ta sake fitar da sabbin sharuɗa 15 na buɗe wuraren bauta

Gwamnatin Tarayya ta sake fitar da sabbin sharuɗa 15 na buɗe wuraren bauta

A fafutikar da gwamnatin Najeriya ke yi na dakile yaduwar cutar korona a kasar, ta sake fidda wasu sabbin sharuɗa da za a kiyaye domin wuraren bauta su ci gaba da kasancewa a buɗe.

Kwamitin shugaban kasa mai yaki da cutar korona PTF, shi ne ya sabunta matakan kariya da suka kunshi sabbin sharuɗa da za a kiyaye a masallatai da majami'u.

Ma'aikatar lafiya ta tarayya, ta sanar da cewa wannan sabbin matakan za su taka muhimmiyar rawar gani wajen dakile yaduwar cutar korona a kasar.

Kwamitin shugaban kasa mai yaki da cutar korona
Kwamitin shugaban kasa mai yaki da cutar korona
Asali: Twitter

Ga jerin ka'idodin kariya 17 da aka shata wa masallatai:

  1. Salloli biyar na yau da kullum da sallar juma'a ne kawai aka ba da izinin gudanarwa a masallatai.
  2. Kada a haura awa daya wajen gudanar da sallar Juma'a tare da hudubarta
  3. Tsatace dukkanin harabar masallaci, famfo, marikin kofa, da makunnan fitilu da fanka
  4. Wajibi ne amfani da takunkumin rufe fuska ga dukkan masallata
  5. Samar da wuraren wanke hannu a karkashin ruwa mai gudana da kuma abin daukar zafin jiki.
  6. Ba a son mutane su rika gaisawa da juna, sumbata, ko rungumar juna.
  7. Sanya alamomin tunatar da mutane a kan yin nesa-nesa da juna.
  8. Tanadar akwatin jefa sadaka a kowace mashiga ta masallatai.
  9. Samar da ruwa da kuma wurin yin alwala.
  10. Sanya alamomin bayar da tazara a kan daɓe ko shimfidar masallatai.
  11. Kada a rika cudanya wajen amfani da Qur'ani, abin shimfida ko butar alwala.
  12. Babu taron jama'a gabani ko bayan an kammala ibada.
  13. A tabbatar da tsaftar makewayi da bandakuna.
  14. Rufe duk wani saye da sayarwa a harabar masallaci.
  15. An shawarci tsofaffi masu rauni da ke fama da wasu cututtukan kamar ciwon suga da ciwon zuciya da su rika sallolinsu a gida.
  16. Makarantun Islamiya, Tahfizu, da Makarantun dare za su ci gaba da kasancewa a rufe
  17. Ana son iska ta wadata saboda haka dole a bude kofa da tagogi a duk lokacin gudanar da ibada a wuraren bauta.

KARANTA KUMA: Mutanen da cutar korona ta harba a Najeriya sun zarta 24, 000 - NCDC

Ga jerin ka'idodin kariya 17 da aka shata wa cocika:

  1. A ranar Lahadi kadai za a buɗe coci
  2. Za a buɗe coci daga karfe 5.00 na safe zuwa 8.00 na dare
  3. A rika bayar da tazara ta awa daya bayan kowane taron masu bauta
  4. Tsatace dukkanin harabar coci, kofofi, marikin kofa, da makunnan fitilu da lasifika
  5. Samar da wuraren wanke hannu a karkashin ruwa mai gudana da kuma abin daukar zafin jiki.
  6. Wajibi ne amfani da takunkumin rufe fuska ga dukkan masu bauta
  7. Sanya alamomin tunatar da rashin gaisawa da juna, sumbata, ko rungumar juna.
  8. Tanadar akwatin jefa sadaka a kowace mashiga ta coci.
  9. Sanya alamomin bayar da tazara a kan daɓen coci.
  10. Babu taron jama'a gabani ko bayan an kammala ibada.
  11. A tabbatar da tsaftar makewayi da bandakuna.
  12. Rufe duk wani saye da sayarwa a harabar coci.
  13. An shawarci tsofaffi masu rauni da ke fama da wasu cututtukan kamar ciwon suga da ciwon zuciya da su rika sallolinsu a gida.
  14. A tabbatar da iska ta wadata a wurin bauta.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel