Adadin masu cutar korona a Afirka ya zarta 330,000 - WHO

Adadin masu cutar korona a Afirka ya zarta 330,000 - WHO

- Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce an samu mutum fiye da mutum 330,000 da suka kamu da Coronavirus a nahiyar Afirka

- Hukumar ta ce fiye da mutum 160,000 sun warke yayin da sama da mutum 8,800 suka mutu sakamakon annobar

- Rahoton da WHO ta wallafa ya nuna cewa mutum 111,796 sun kamu a Afirka ta Kudu, 22,020 a Najeriya, sai kuma 12,248 a Algeria

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, a ranar Alhamis, 25 ga watan Yuni, ta sanar da cewa cutar korona ta harbi sama da mutane 330,000 a nahiyar Afirka.

Reshen Hukumar WHO na Afrika da ke birnin Brazzaville a kasar Congo, shi ne ya fitar da wannan sanarwa a kan shafin dandalin sada zumunta na Twitter.

Sanarwar ta bayyana cewa, cutar korona ta harbi mutum 335,791 a nahiyar Afirka, kuma an samu mutum 160,829 da suka warke bayan kamuwa da cutar.

Haka kuma alkaluman da Hukumar ta fitar sun nuna cewa, an samu mutum 8,856 da cutar korona ta hallaka a baki daya nahiyar Afrika.

Shugaban Hukumar WHO na Duniya; Tedros Adhanom
Shugaban Hukumar WHO na Duniya; Tedros Adhanom
Asali: UGC

Kididdigar ta nuna cewa, kasar Afrika ta Kudu, Najeriya da kuma Algeria, sun fi sauran kasashen nahiyar yawan mutanen da cutar ta harba.

Cikin rahoton, Afirka ta Kudu tana da mutum 111,796 da suka kamu da cutar, sai kuma mutum 2,205 da cutar ta hallaka.

KARANTA KUMA: Kwayar Tramadol tana kara rura wutar ta'addanci a Arewa maso Gabas - NDLEA

A Najeriya cutar ta harbi mutum 22,020, sannan kuma an tabbatar da mutuwar mutum 542 a kasar.

Sai kuma kasar Aljeriya inda alkaluma suka tabbatar da kamuwar mutane 12,248, yayin da mutane 869 suka riga mu gidan gaskiya.

Ga jerin adadin mutanen da cutar korona ta harba cikin kowace kasa a nahiyar Afrika

Algeria – 12,248

Angola – 197

Benin – 902

Botswana – 92

Burkina Faso – 919

Burundi – 144

Cameroon – 12,592

Cape Verde – 999

Central African Republic – 3,099

Chad – 860

Comoros – 265

Congo-Brazzaville – 1,087

DR Congo – 6,213

Djibouti – 4,630

Egypt – 59,561

Equatorial Guinea – 1,664

Eritrea – 144

Eswatini – 690

Ethiopia – 5,034

Gabon – 4,956

(The) Gambia – 42

Ghana – 15,013

Guinea – 5,174

Guinea-Bissau – 1,556

Ivory Coast – 8,164

Kenya – 5,206

Lesotho – 17

Liberia – 662

Libya – 670

Madagascar – 1,787

Malawi – 941

Mali – 2,005

Mauritania – 3,519

Mauritius – 341

Morocco – 10,907

Mozambique – 762

Namibia – 76

Nijar – 1,051

Najeriya- 22,020

Rwanda – 830

Sao Tome da Principe – 710

Senegal – 6,129

Seychelles – 11

Sierra Leone – 1,354

Somalia – 2,835

Afrika ta Kudu – 111,796

Sudan ta Kudu – 1,942

Sudan – 8,889

Tanzania – 509

Togo – 583

Tunisia – 1,160

Uganda – 805

Zambia – 1,489

Zimbabwe – 530

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel