Yanzu-yanzu: Sabbin mutum 649 sun kamu da cutar korona a Najeriya

Yanzu-yanzu: Sabbin mutum 649 sun kamu da cutar korona a Najeriya

Alkalumman hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa na ranar Laraba, 24 ga watan Yuni, ya bayyana cewa mutum 649 sun sake kamuwa da cutar korona a Najeriya.

A jihar Legas an samu sabbin masu cutar 250, jihar Oyo an samu karin mutum 100 sai jihar Filato an samu karin mutum 40 da ke dauke da cutar.

A jihar Delta an samu karin mutum 40 sai jihar Abia inda aka samu karin mutum 28 yayin da aka samu karin mutum 27 a jihar Kaduna.

A jihar Ogun an samu karin mutum 22, jihar Edo an samu karin mutum 20, sai kuma jihar Akwa Ibom inda aka samu karin mutum 18.

A jihar Kwara an samu karin mutum 17, babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja an samu sabbin masu cutar har 17 yayin da jihar Enugu ta samu karin mutum 14.

A jihohin Neja da Adamawa an samu karin mutum goma sha uku-uku, sai jihar Bayelsa an samu sabbin mutum 7 da ke dauke da cutar.

Jihohin Osun da Bauchi sun samu karin mutum shida-shida sai jihar Anambra da ke da karin mutum hudu.

A jihar Gombe akwai karin mutum 3, yayin da jihar Sokoto ta samu karin mutum biyu. Jihohin Imo da Kano sun samu karin mutum daddaya.

Jimillar masu cutar a Najeriya ta kai 22,020 yayin da mutum 7613 aka sallamesu daga asibiti. Mutum 542 suka riga mu gidan gaskiya sakamakon cutar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng