Jerin 'yan majalisar wakilai da suka fi kawo kudirorin samar da ci gaba a kasa

Jerin 'yan majalisar wakilai da suka fi kawo kudirorin samar da ci gaba a kasa

An yanke hukuncin cewa, Abbas Tajuddeen da Tahir Monguno, su ne 'yan majalisar wakilai guda biyu da suka fi sa'o'insu kawo mafi yawan kudirori domin ci gaban kasa.

Honarabul Tajuddeen wanda ya ke wakiltar mazabar Zaria a zauren majalisar tarayya, ya kawo kudirori 59, yayin da takwaransa Monguno na jihar Borno, ya kawo kudirori 40.

Kamar yadda rajistar majalisar dokoki ta tarayya ta nuna, Femi Gbajbiamila, kakakin majalisar wakilai na yanzu, ya fi kowane dan majalisa kawo yawan kudirorin da tuni an shigar da su cikin doka.

Sauran 'yan majalisar da suka kawo tarin kudirori domin ci gaban kasa sun hadar da:

Nkeiruka Onyejeocha (APC Abia) - Kudirori 19

Nkem Abonta (Abia) - Kudirori 30

Ossai Nicholas Ossai (Delta) - Kudirori 29

Dachung Bagos (Plateau) - Kudirirrika 27

Simon Nwadkwom (Plateau) - Kudirori 22

Francis Uduyok (Akwa Ibom) - Kudirori 15

Gideon Gwani (Kaduna) - Kudirori 15

Femi Gbajabiamila (Lagos) - Kudirori 17

Zauren majalisar wakilai
Zauren majalisar wakilai
Asali: Facebook

Daga cikin kudirori 17 da Gbajabiamila ya kawo, tuni majalisar wakilai ta shigar da shida cikin doka, yayin da ragowar da suka hadar da yi wa kundin tsarin mulkin kasa kwaskwarima ke jiran sakamakon binciken kwamiti.

Haka kuma, daga cikin kudirori 59 da Honarabul Tajuddeen ya kawo zauren majalisar, 22 sun kasance na neman a samar da cibiyoyin Lafiya na Tarayya ne a wasu jihohi 21 da ke fadin kasar.

A wani rahoton mai nasaba da wannan da jaridar Legit.ng ta ruwaito, majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin da ya nemi a rika dandake mutanen da aka kama da laifukan fyade a kasar nan.

KARANTA KUMA: Babu wata jiha a Najeriya da ta tsarkaka daga cutar korona - NCDC

Tun farko dai dan majalisar wakilai daga jihar Lagos, James Abiodun Faleke, shi ne ya gabatar da kudirin, inda ya nemi a rika dandake mutanen da aka kama sun aikata laifukan fyade.

Sai dai majalisar ta amince da a shimfida tsauraran hukunce-hukunce kan mutanen da aka kama da laifin fyade.

Majalisar ta cimma matsayar hakan ne yayin zaman da ta gudanar a ranar Alhamis, 4 ga watan Yuni, bayan kiraye-kirayen da aka yi sakamakon yawaitar rahotannin fyade da ake samu a kasar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel