Kasashe 8 masu karfin tattalin arziki a Afrika

Kasashe 8 masu karfin tattalin arziki a Afrika

- A 2019 an yi kiyasin cewa Najeriya ce ke ta fi kowacce kasa karfin tattalin arziki a Afrika da $444.916 biliyan

- Kasashe irinsu Algeria, Angola da Morocco ne a matakai na hudu, bakwai da biyar

- Kasar Afrika ta Kudu da Egypt ne suka bayyana da $371.298 biliyan da $299.589 biliyan

Najeriya ce ta daga a kasashe masu karfin tattalin arziki a dukkan Afrika a 2019 kamar yadda Africa Facts Zone ta wallafa.

A wata wallafa da tayi a shafinta na Twitter a ranar Juma'a, 5 ga watan Yuni, Najeriya ce ke kan gaba da karfin tattalin arziki da ya kai $444.916 biliyan.

Kasar Afrika ta Kudu ce ta bayyana a ta biyu da $371.29 biliyan yayin da Egypt ta kai mataki na uku da $299.589 biliyan.

Kasar Kenya na a ta hudu da $99.246 biliyan, Angola ta biyar da $92.191 biliyan sai kuma Ethiopia da ke da $90.968.

KU KARANTA: Abubuwa 6 masu bada mamaki game da Najeriya

Kasashe 8 masu karfin tattalin arziki a Afrika
Kasashe 8 masu karfin tattalin arziki a Afrika. Hoto daga Al-Jazeera
Asali: Twitter

A wani labari na daban, annobar korona ta shafi duk wani bangare na tattalin arzikin duniya da kasuwanci. Amma duk da haka, mujallar Forbes ta wallafa manyan masu kudi a duniya da suka kai 2,095.

Ga manyan masu kudin duniya da takaitaccen bayani a kansu.

1. Jeff Bezos: Dan asalin kasar Amurka ne kuma ya samu kudinsa ta fasahar Amazon. Bezos ya mallaki dukiya da ta kai $113 biliyan. Shine ya fi kowanne mahaluki kudi a duniya a shekarar 2020.

2. Bill Gates: Dan asalin kasar Amurka ne kuma shi ke da fasahar Microsoft. Bill Gates ya mallaki dukiyar da ta kai $98 biliyan kuma shine mutum na biyu da ya fi kowa arziki a duniya a 2020.

3. Bernard Arnault & Family: Hamshakin mai kudin ya mallaki dukiyar da ta kai $76 biliyan kuma dan kasar Faransa ne.

4. Warren Buffett: Hamshakin mai arzikin ya mallaki dukjya da ta kai $67.5 biliyan. Dan asalin kasar Amurka ne mamallakin Berkshire Hathaway Finance & Investment.

5. Larry Ellison: Mai tarin dukiya ne da ya bayyana a mataki na biyar a fadin duniya. Ya mallaki dukiyar da ta kai $57 biliyan. Dan asalin kasar Amurka ne.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng