Tsohon alkalin kotun kolin Najeriya, Karibi, ya rasu

Tsohon alkalin kotun kolin Najeriya, Karibi, ya rasu

Tsohon alkalin kotun koli, Adolphus Karibi-Whyte ya rasu yana da shekaru 88. Dan alkalin, Dagogo Karibi-Whyte ne ya tabbatar da mutuwar mahaifin nasa a garin Fatakwal, babban birnin jihar Rivers.

An haifa dan asalin Abonnema din da ke jihar Rivers a ranar 29 ga watan Janairun 1932.

Ya halarci kwalejin Kalabari da ke Buguma a jihar Rivers daga 1946 zuwa 1959 kuma ya yi aiki a matsayin kilakin kotu daga 1951 zuwa 1957.

Ya samu digirinsa a fannin shari'a daga jami'ar Hull da ke Ingila a 1960 kuma an rantsar da shi a matsayin lauya a shekarar da ta zagayo.

A watan Satumban 1962, ya samu digirinsa na biyu a fannin shari'a daga jami'ar Landan. A shekarar 1970 ya samu digirin-digirgir a fannin shari'a daga jami'ar jihar Legas.

An nada marigayin a matsayin alkalin kotun hukumar kudin shiga ta tarayya a 1976.

An kara masa matsayi zuwa kotun daukaka kara a 1980 kuma daga baya ya koma kotun kolin Najeriya a 1984.

Wasu daga cikin manyan shari'un da ya yanke hukunci kuma ya samu jinjina a Najeriya sun hada da: Shari'ar gwamnatin jihar Gongola da Tukur a 1989, shari'ar Antoni janar din tarayya da Antoni Janar din jihar Abia.

Tsohon alkalin kotun kolin Najeriya, Karibi, ya rasu
Tsohon alkalin kotun kolin Najeriya, Karibi, ya rasu. Hoto daga The Nation
Asali: Twitter

KU KARANTA: An damke malamin da ya yi wa El-Rufai 'wankin babban bargo' a kan hana sallar Idi

Ya yi shari'ar Grace Jack da jami'ar aikin noma da ke Makurdi a 2004 da kuma shari'ar bankin Savannah da Pan Atlantic shipping da Transport Agencies Limited a 1987.

Tsohon alkalin ya rasu ya bar 'ya'ya bakwai.

A wani labari na daban, Sheikh Bello yabo dan asalin jihar Sokoto ya shiga hannun jami'an tsaro tun bayan bazuwar bidiyon da ya caccaki gwamnan Kaduna a kan hana sallar Idi.

A wani sautin murya mai tsayin kusan minti biyar, malamin addinin Islama mai suna Sheikh Bello Yabo, ya caccaki Gwamna Malam Nasir El-Rufai saboda hana sallar Idi da yayi a jihar Kaduna.

A sautin muryar, ya yi kira ga Musulmi da su bijirewa hukumomi a kowanne gari da aka hana su fita sallar Idin karamar sallar don dakile yaduwar cutar korona, kamar yadda jaridar SaharaReporters ta ruwaito.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel